• Leadership Hausa
Monday, May 29, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Abubuwa 10 Da Zaku So Sani Cikin Jawabin Bankwana Da Buhari Ya Yi Wa ‘Yan Nijeriya

Ganduje Zai Mika Wa Abba Gida-Gida Ragamar Mulkin Kano, Don Halartar Rantsar Da Tunibu

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce yana shirin barin gidan gwamnati domin ya koma gidansa, yana aiki a gonakinsa da kiwon dabbobinsa sama da 300.

“Na kosa in bar gidan gwamnati,” in ji Buhari yake bayyana haka a fadar gwamnati da ke Abuja ranar Talata yayin da yake karbar jakadiyar Amurka, Mary Beth Leonard mai barin gado.

  • ‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023
  • Shema Ya Bai Wa PDP Sa’o’i 48 Ta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Masa

Ya ce idan aka yi la’akari da damar gudanar da zabe na gaskiya da kuma rashin tsoma baki kamar yadda aka gani a zabukan ranakun 25 ga Fabrairu da 18 ga Maris, ‘yan Nijeriya sun tabbatar da cewa sun iya tantance wanda zai jagorance su ba tare da wani ya gaya musu abin da za su yi ba.

Ya nuna jin dadinsa da gagarumin kishi ga dimokuradiyya da ‘yan Nijeriya ke nunawa ta zabin da suka yi a zaben 2023.

A cewar shugaban, wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Garba Shehu, ya fitar, ya ce da gaske dimokuradiyyar Nijeriya ta girma.

Ya ce: “Mutane sun fahimci ‘yancin da suke da shi. Idan aka ba da damar yin zabe na gaskiya da gaskiya, babu wanda zai iya gaya musu abin da zai yi. Ban ji dadin yadda wasu ‘yan takara suka fadi zabe ba.

“Amma na ji dadin yadda masu jefa kuri’a suka iya yanke zabar ra’ayinsu na wanda zai yi nasara da kuma wanda zai fadi. Duk da canjin kudin na rage zirga-zirgar kudade a hannun jama’a, amma sai da wasu suka raba kudin, na ce wa masu kada kuri’a su karbi kudin su yi zabi ra’ayinsu”

Ya ce ya gamsu da irin rawar da ya taka wajen gudanar da zaben ya tsaya a kansa, ba tare da tsoma baki ko wani tsangwama ba.Ya yaba wa jakadan mai barin gado cewa bisa ga dimbin nasarorin da aka samu a dangantakar Nijeriya da Amurka cikin shekara uku da rabi. Ya bayyana fatan Nijeriya za ta ci gaba da samun ci gaba wajen gina kasa daga cikin al’ummominmu daban-daban da masu fafutuka.

Tun da farko, Leonard ta bukaci a cire tallafin mai ya daga cikin muhimman shawarwarin da Buhari zai iya dauka kafin ya bar mulki a ranar 29 ga Mayu.

Ta ce ta yi farin ciki da irin ci gaban da aka samu a dangantakar Nijeriya da Amurka a cikin shekaru uku da rabi, musamman yadda aka kafa kwanan nan na tsarin bayar da biza na tsawon shekaru biyar tsakanin kasashen biyu, aiki tare a cikin tsaro da samar da kayan aikin soji da suka hada da jiragen yaki da jirage masu saukar ungulu na yaki masu zuwa nan ba da dadewa ba, da kuma hadin gwiwa a fannin kiwon lafiya don yaki da cutar kanjamau da kuma Korona tare da ba da tabbacin cewa Amurka za ta ci gaba da taimakawa wajen karfafa fannin kiwon lafiya a Nijeriya.

Ta bayyana godiyarta da na gwamnatin Amurka kan ci gaba da rawar da shugaban kasar ke takawa wajen tabbatar da tsaro a yankin Afirka da kuma karfafa tsarin dimokuradiyya a matsayin tsarin gwamnati, inda ta bayyana irin kakkausan martanin da ya bayar kan yawaitar juyin mulkin da aka yi a yammacin Afirka a baya-bayan nan a matsayin wanda bai dace ba.

Tags: BuhariZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Ta Yi Mun Daidai Da Ta Ayyana Zaɓen Gwamnan Adamawa Bai Kammalu Ba – Binani

Next Post

Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

Related

Abubuwa 10 Da Zaku So Sani Cikin Jawabin Bankwana Da Buhari Ya Yi Wa ‘Yan Nijeriya
Manyan Labarai

Abubuwa 10 Da Zaku So Sani Cikin Jawabin Bankwana Da Buhari Ya Yi Wa ‘Yan Nijeriya

1 day ago
Ganduje Zai Mika Wa Abba Gida-Gida Ragamar Mulkin Kano, Don Halartar Rantsar Da Tunibu
Manyan Labarai

Ganduje Zai Mika Wa Abba Gida-Gida Ragamar Mulkin Kano, Don Halartar Rantsar Da Tunibu

1 day ago
Na Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Na Same Ta A 2015 – Buhari
Manyan Labarai

Na Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Na Same Ta A 2015 – Buhari

1 day ago
An Ci Gaba Da Jefa Kuri’a A Zaben Turkiyya Zagaye Na Biyu A Yau Lahadi
Manyan Labarai

An Ci Gaba Da Jefa Kuri’a A Zaben Turkiyya Zagaye Na Biyu A Yau Lahadi

1 day ago
Ba Ma Kokarin Musuluntar Da Nijeriya –Shettima
Manyan Labarai

Ba Ma Kokarin Musuluntar Da Nijeriya –Shettima

2 days ago
Kwankwaso Ba Zai Sauya Jam’iyya Ba -NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sauya Jam’iyya Ba -NNPP

2 days ago
Next Post
Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

LABARAI MASU NASABA

An Rantsar Da Gwamna Bala Muhammad A Matsayin Gwamnan Bauchi A Karo Na 2

An Rantsar Da Gwamna Bala Muhammad A Matsayin Gwamnan Bauchi A Karo Na 2

May 29, 2023
Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

Jagoranci Za Mu Yi Ba Mulkin ‘Yan Nijeriya Ba – Tinubu

May 29, 2023
Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

May 29, 2023
Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

May 29, 2023
A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

May 29, 2023
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

May 29, 2023
Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

May 29, 2023
Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

May 29, 2023
Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

May 29, 2023
Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

May 28, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.