ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Buhari

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce yana shirin barin gidan gwamnati domin ya koma gidansa, yana aiki a gonakinsa da kiwon dabbobinsa sama da 300.

“Na kosa in bar gidan gwamnati,” in ji Buhari yake bayyana haka a fadar gwamnati da ke Abuja ranar Talata yayin da yake karbar jakadiyar Amurka, Mary Beth Leonard mai barin gado.

  • ‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023
  • Shema Ya Bai Wa PDP Sa’o’i 48 Ta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Masa

Ya ce idan aka yi la’akari da damar gudanar da zabe na gaskiya da kuma rashin tsoma baki kamar yadda aka gani a zabukan ranakun 25 ga Fabrairu da 18 ga Maris, ‘yan Nijeriya sun tabbatar da cewa sun iya tantance wanda zai jagorance su ba tare da wani ya gaya musu abin da za su yi ba.

Ya nuna jin dadinsa da gagarumin kishi ga dimokuradiyya da ‘yan Nijeriya ke nunawa ta zabin da suka yi a zaben 2023.

A cewar shugaban, wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Garba Shehu, ya fitar, ya ce da gaske dimokuradiyyar Nijeriya ta girma.

Ya ce: “Mutane sun fahimci ‘yancin da suke da shi. Idan aka ba da damar yin zabe na gaskiya da gaskiya, babu wanda zai iya gaya musu abin da zai yi. Ban ji dadin yadda wasu ‘yan takara suka fadi zabe ba.

“Amma na ji dadin yadda masu jefa kuri’a suka iya yanke zabar ra’ayinsu na wanda zai yi nasara da kuma wanda zai fadi. Duk da canjin kudin na rage zirga-zirgar kudade a hannun jama’a, amma sai da wasu suka raba kudin, na ce wa masu kada kuri’a su karbi kudin su yi zabi ra’ayinsu”

Ya ce ya gamsu da irin rawar da ya taka wajen gudanar da zaben ya tsaya a kansa, ba tare da tsoma baki ko wani tsangwama ba.Ya yaba wa jakadan mai barin gado cewa bisa ga dimbin nasarorin da aka samu a dangantakar Nijeriya da Amurka cikin shekara uku da rabi. Ya bayyana fatan Nijeriya za ta ci gaba da samun ci gaba wajen gina kasa daga cikin al’ummominmu daban-daban da masu fafutuka.

Tun da farko, Leonard ta bukaci a cire tallafin mai ya daga cikin muhimman shawarwarin da Buhari zai iya dauka kafin ya bar mulki a ranar 29 ga Mayu.

Ta ce ta yi farin ciki da irin ci gaban da aka samu a dangantakar Nijeriya da Amurka a cikin shekaru uku da rabi, musamman yadda aka kafa kwanan nan na tsarin bayar da biza na tsawon shekaru biyar tsakanin kasashen biyu, aiki tare a cikin tsaro da samar da kayan aikin soji da suka hada da jiragen yaki da jirage masu saukar ungulu na yaki masu zuwa nan ba da dadewa ba, da kuma hadin gwiwa a fannin kiwon lafiya don yaki da cutar kanjamau da kuma Korona tare da ba da tabbacin cewa Amurka za ta ci gaba da taimakawa wajen karfafa fannin kiwon lafiya a Nijeriya.

Ta bayyana godiyarta da na gwamnatin Amurka kan ci gaba da rawar da shugaban kasar ke takawa wajen tabbatar da tsaro a yankin Afirka da kuma karfafa tsarin dimokuradiyya a matsayin tsarin gwamnati, inda ta bayyana irin kakkausan martanin da ya bayar kan yawaitar juyin mulkin da aka yi a yammacin Afirka a baya-bayan nan a matsayin wanda bai dace ba.

Buhari
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Ta’addanci
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Next Post
Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

July 9, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

July 9, 2026
An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

July 9, 2026
kebbi

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Shugabar Namibia

Li Qiang Ya Gana Da Shugabar Namibia

July 9, 2026
Xi Ya Bayar Da Umarni Dangane Da Gobarar Da Ta Tashi A Wani Kamfanin Sarrafa Takalma Dake Gabashin Kasar

Xi Ya Bayar Da Umarni Dangane Da Gobarar Da Ta Tashi A Wani Kamfanin Sarrafa Takalma Dake Gabashin Kasar

July 9, 2026
Ta’addanci

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.