• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Buɗe Cibiyar Fasfo Ta Zamani Da Za Ta Karaɗe Jihohin Edo Da Delta

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
Fasfo

Daga dama: Kwanturolar NIS ta Edo, Rabi Garba, Gwamna Obaseki na Edo, Minista Aregbesola, Shugaban NIS CGI ISah Idris Jere da ACG Domnic Asogwa yayin bude cibiyar ta fasfo

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta ƙaddamar da cibiyar bayar da ingataccen fasfo na zamani da za ta karaɗe jihohin Edo da Delta.

Hukumar ta ƙaddamar da cibiyar ce a ranar Talatar nan bisa jagorancin Ministan Cikin Gida Rauf Ogbeni Aregbesola da Shugaban NIS, CGI Isah Idris Jere.

Fasfo
CGI Isah Idris yayin da aka tarbe shi a Benin yayin kaddamarwar

Sanarwar da Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, ACI Amos Okpu ya fitar, ta bayyana cewa, da yake ƙaddamar da cibiyar, Minista Aregbesola ya ce cibiyar za ta dinga biyan buƙatun masu neman fasfo da suka fito daga yankunan jihohin Edo da Delta.

Ministan ya ƙara da cewa, cibiyar za ta kasance ta musamman da za ta kula da ofishoshin fasfo na jihohin guda biyu, saboda ƙara inganta ayyukan samar da fasfo a waɗannan jihohi.

  • Tawagar NIS Ta Kai Ziyarar Aiki A Poland Kan Tsaron Iyakoki

Ya ƙara da cewa bisa ƙaddamar da cibiyar, ofisoshin fasfo na jihohin Edo da Delta za su yi aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran wurare da ke yankin kudu maso gabas da kudu maso yamma wajen samun nasarar bunƙasa ɓangaran fasfo na zamani.

Labarai Masu Nasaba

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

Fasfo
CGI Isah Idris Jere (na farko a dama) da sauran manyan baki a fadar Oba na Benin

Minstan ya ce inganta fasfo na zamani wata dama ce da masu buƙatar za su zaɓi nau’in fasfo da suke muradi, kamar mai feji 32 da ke aiki na tsawon shekaru biyar da mai feji 64 da ke aiki na tsawon shekaru biyar da kuma mai feji 64 da ke aiki na tsawon shekaru 10.

Ya ce inganta harkokin fasfo zuwa na zamani hanya ce ta ƙara bunƙasa fasaha, musamman inganta sha’anin taro ta yadda kundayen hukumar da ke ɗauke da bayanai za su yi wahalar kwaikwayo da buga na jabu.

A cewarsa, an samar da wannan cibiya ce domin sauƙaƙa wa masu neman tare da kauce wa wahalar da su zuwa wuri main isa a duk lokacin da suka buƙaci samun fasfo, ta yadda za su yi amfani da na’urar zamani wajen gabatar da buƙatarsu ta samun fasfo cikin kwanciyar hanhali a gidajensu ko kuma a ofishinsu.

Fasfo
Minista Aregbesola yayin da yake kaddamar da ofishin fasfon

Ministan ya jaddada cewa gwamnati tana ƙara wasu shirye-shirye wajen tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya suna samun fasfo cikin sauƙi ba tare da wata wahala ba.

A nasa jawabin, Kwanturola Janar na Hukumar NIS, Isah Jere Idris ya bayyana cewa samar da cibiyar ingantaccen fasfo na zamani da ke Benin na ɗaya daga cikin ƙoƙarin sauye-sauyen da yake aiwatarwa a ɓangaren, musamman wajen ƙara faɗaɗa wa masu neman fasfo hanyoyin samu da kuma zaɓi a kan irin wanda suke muradi.

Ya buƙaci masu neman fasfo da su ziyarci shafin hukumar na intanet a passport.immigration.gov.ng a kowani lokaci, domin biyan kuɗaɗe da kuma gabatar da buƙatar neman fasfo tun kafin lokaci ya ƙure, domin kaucewa cunkoso lokacin da suke buƙata.

Ya ƙara da cewa hukumar ba ta amince da biyan tsabar kuɗi ba, inda ya yi kira da masu nema da su tabbatar sun biya kuɗaɗensu ta shafin intanet tun kafin su ziyarci ofisoshin fasfo lokacin da aka tsara musu.

Tun da farko dai, Gwamnan Jihar Edo, Mista Godwin Noheghase Obaseki ya yaba wa hukumar NIS bisa samar da waɗannan sauye-sauye wajen bayar da fasfo. Ya nuna jin daɗinsa wajen zaɓar garin Benin a matsayin cibiya ta wannan aiki, inda ya sha alwashin cewa gwamnatinsa za ta bayar da duk wata gudummuwa da hukumar take buƙata ciki har da tabbacin goyon bayan ƙudurin aikin gina ofishin fasfo a Auchi.

Fasfo
Minista Aregbesola yana jawabi a fadar Oba na Benin

Bugu da ƙari, Sarkin Benin, Mai Martaba Omo no’ Oba n’Edo Uku Akpolokpolo, Oba Ewuare II, Ogidigan ya yaba wa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari bisa amincewa da kafa cibiyar ingantaccen fasfon na zamani a masarautarsa. Ya ƙara da cewa shugaban ƙasa ya daɗe yana faranta wa mutanen Jihar Edo rai da kuma ‘yan Nijeriya gaba ɗaya.

Ya tabbatar da cewa zai bayar da goyon baya kan wannan aiki tare da miƙa godiyarsa ga Ministan Harkokin Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola bisa jagorantar manyan jami’an hukumar NIS da kuma sauran ma’aikatu da suka zo yankinsa.

  • https://passport.immigration.gov.ng/

A cikin waɗanda suka halarci ƙaddamar da katafariyar cibiyar ta fasfo har da Hon. Justice PA Akhikhero wanda ya wakilci Alƙalin-alƙalai na jihar, da shugaban ma’aikatan gwamna da muƙaddashin shugaban jami’ar Ambrose Alli, Farfesa Osarheme Osadolor, da shugabannin rundunar sojojin Nijeriya da sauran jami’an tsaro.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina Jin Takaici Da Damuwa Kan Yadda Ake Fita Daga Jam’iyyarmu Ta APC —Abdullahi Adamu

Next Post

Al’umar Mai’adua Na Bukatar Gyaran Masallacin Juma’arsu Da Ya Shafe Shekaru Ba Gyara

Related

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 
Manyan Labarai

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

21 minutes ago
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

13 hours ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

15 hours ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

16 hours ago
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

18 hours ago
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

19 hours ago
Next Post
Al’umar Mai’adua Na Bukatar Gyaran Masallacin Juma’arsu Da Ya Shafe Shekaru Ba Gyara

Al'umar Mai'adua Na Bukatar Gyaran Masallacin Juma'arsu Da Ya Shafe Shekaru Ba Gyara

LABARAI MASU NASABA

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.