• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudu Zuwa Kasashen Waje: Gwamnati Na Shirin Taka Wa Likitoci Birki

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gudu Zuwa Kasashen Waje: Gwamnati Na Shirin Taka Wa Likitoci Birki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da yawan ‘yan Nijeriya ke karuwa kullum sai ga shi kuma kwararrun ta banagen kiwon lafaiya suna kara raguwa,saboda kuwa yadda tsarin kula da marasa lafiya yakamata ya kasance kamar yadda kudurin hukumar lafiya ta duniya ya bayyana na Likita  daya ya lura da marasa lafiya 1,000 yanzu al’amarin ya kasance ne na likita 1 ya duba marasa lafiya 10,000 a Nijeriya

Yadda kwararrun da suka shafi kula da lafiyar al’umma suke barin Nijeriya hakan ba karamin cikas yake kawo ma bangaren kula da lafiyar al’umma ba, yanzu kalilan wadanda kware a bangaren kula da lafiyar al’umma suke rage a Nijeriya,domin su kula da lafiyar ‘yan Nijeriya.

  • Sallah: Gwamna Bagudu Ya Umarci A Biya Albashin Watan Afrilu
  • INEC Ta Raba Muhimman Kayyayakin Zabe Don Kammala Zaben Gwamnan Kebbi

Alkalumman da ake dasu sun nuna Nijeriya ta rasa fiye da Likitoci 9,000 da suka barta zuwa kasashen Ingila, Kanada, da kuma Amurka tsakanin shekarun 2016 da 2018.Hakanan ma Likitoci 727 wadanda suka kware a Nijeriya suka koma Ingila kadai cikin wata shida, tsakaniu watannin Disamba  2021 da Mayu 2022.

Alkalumman da aka samu daga cibiyar kula da aikin Nas da Unguwar zoma ta Ingila ta nuna ‘yan Nijeriya da aka koya masu suka kware daga aikin, ya nuna wadanda suke barin sun karu da kashi  68.4 ko daga2,790 a watan Maris na 2017 zuwa 7,256  na watan Maris 2022.”

Da yake tabbatar  da hakan  shugaban kungiyar Likitoci na kasa (MDCAN),yace bada dadewa ba Nijeriya tana daukar kawi Likitoci kashi 30 na 4000 da ake yayewa ko wace shekara a Nijeriya.Kamar yadda shugaban na kungiyar ta Likitoci, Doctor Bictor Makanjuola cewa yayi, “Muna daukar kashi 30 daga cikin wadanda muka sake horarwa 4,000 ko wace shekara”

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Makanjuola ya ce muna daukar kashi 30 na kwararru wadanda muke sake horarwa duk da yake Nijeriya ta sake shiga cikin matsalar za kuma ta cigaba da fuskantar hakan, har sai idan an dauki matakan daya kamata.

Ya kara jaddada cewa “Idan muka dauki kashi 30 na 12,000 hakan shi yafi fiye da kashi na4,000.idan kuma muka horar dai 12,000,kashi 30 shi yafi kyau fiye da wadanda ake dasu a halin yanzu na kusan 4,000.Da hakan mu kesa ran taimaka ma shi al’amarin ba kamar yadda ya dace ba amma a kalla dai ana cigaba da yin tsarin.”

Halin da ake ciki yanzu dokar hana hana Likitoci da Likitocin Hakora barin Nijeriya ta tsallake karatu na biyu a zaman majalisarWakilai ta kasa, har sai sun yi shekara biyar.

Kudurin dokar wanda Ganiyu Abiodun Johnson ya gabatar mai taken, “ Kuduri mai niyyar ayi gyara a dokar Likitoci da Likitocin Hakora ta kasa, mai lamba ta Cap M379,ta dokokin Nijeriya  shekara ta 2004 domin yin duk wani gyara domin a sa duk wani wanda ya aka horar a matsayin Likitan Hakora ko Likita sai ya yi shekara biyar tukuna kafin a amince ma shi wajen bashi cikakken lasi wanda kungiyar ce zata bada,wannan duk domin a samar da kulawa da lafiyar ‘yan Nijeriya kamar yadda ya dace (HB.2130).

Sai dai kamar yadda ya jaddada Makanjuola cewa yayi “ Hakane shi al’amarin kwararru ta bangaren lafiya yake a kowacce kasar duniya abin ba ya tsaya bane kan Likita,Ko Nas- Nas,da Unguwar-zoma ba,har ma da daukar hotunan wasu cututtuka, da dai sauransu.Duniya tana bukatar kadan daga cikin masu nagarta.

“Babu wanda  zai bari don saboda da kishi kasa kadai zai ki zuwa wurin da za a rika biyan shi har sau goma fiye da abinda ake biyan shi,bayan wannan ma akwai wadansu abubuwa masu bada kwarin gwiwa, sai kuma mutum ya tsaya wurun da ba za a biya shi abinda ya dace ba,wani lokaci abin yayi kasa sosai.Matsalar da muke fuskanta ke nan wannan shi yasa muke ba gwamnati shawara ta kara inganta sharuddan aikin Likitoci da sauran ma’aikatan lafiya,yayin da ta bangaren namu muna yin abinda ya dace na kara  yawan wadanda muke horarwa da yaye su.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaLikitoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masanin Tattalin Arziki: Kasar Sin Ce Karfin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Har Yanzu Wasa Bai Kare Ba, Cewar Thomas Tuchel

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

13 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

1 day ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

2 days ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 days ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Har Yanzu Wasa Bai Kare Ba, Cewar Thomas Tuchel

Har Yanzu Wasa Bai Kare Ba, Cewar Thomas Tuchel

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.