• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Talauci Ya Karu A Nijeriya Da Kashi 14 Cikin 100

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Rahotonni
0
Talauci Ya Karu A Nijeriya Da Kashi 14 Cikin 100
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta fitar da wata kididdiga da ta nuna talauci ya karu a Nijeriya da kashi 14 a cikin 100.

Ta bayyana cewa farashin kayayyakin da ake amfani da su tare da nuna cewa an sami hauhawan farashi da kashi 17.81 a watan Mayu idan aka kwatanta da watan Afrilu da aka sami kashi 16.82 a wannan shekarar duk da yake ya ragu ne a kan abun da aka samu a watan Mayun shekarar da ta gabata ta 2021 da aka sami kashi 17.93.

  • Farashin Kalanzir Da Gas Ya Karu Da Kashi 88 A Cikin Shekara Daya – NBS

Talaudci da kuncin rayuwa a cikin kasa na ta karuwa bisa alamu wanda lamarin ba Nijeriya ba ne kawai duk duniya ne. Bankin Duniya daga baya-bayan nan ya haskako karuwar kuncin rayuwa kusan ilahirin kasashen duniya za su fuskanci wannan matsalar.

Bankin Duniya ya bayyana cewa habakar tattalin arziki ya yi kasa da kashi 2.9 cikin dari daga kashi 5.7 cikin dari da aka hassaso a shekarar 2022. Shugaban Bankin Duniya, Dabid Malpass ya yi gargadin cewa yakin Ukraine da annobar Korona da ya janyo rufe China waDanda suka janyo tashin farashin abinci da sauran kayayyakin bukatun yau da kullum su suka shafi tattalin arziki.

Idan aka duba kyau za a ga cewa kuncin rayuwa ba Nijeriya ne kadai ba, ko’ina ne a duniya, akwai kasashe sama da 25 a duniya da suke da kuncin rayuwa. Alal misali Turkiyyya tana da kuncin rayuwa da kashi 73.5 cikin 100, a yayin da yaki ya kara kuncin rayuwa a Sudan ya karu da kashi 192.2 cikin 100.

Labarai Masu Nasaba

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

Rasha da Ukraine kuncin rayuwa ya karu da kashi 18 da 17 cikin 100, idan aka dawo nan Afrika kuwa, Ethiopia yana da kuncin rayuwa ya kai kashi 37.7 cikin 100. Ghana da Angola da Sierra Leone sun kai kashi 27.6 da 23.42 da 22.44 cikin 100 na kuncin rayuwa.

A lokacin da yake magana kan ci gaba da kuncin rayuwa, Mataimakin Gwamnan babban Bankin Nijeriya a fannin tsarin tattarin arziki, Kingsley Obiora ya ce tattalin arzikin duniya yana tafiya ne cikin wani mawuyacin hali.

Ya ce, “Mun ga yadda farashin kayayyaki suka yi tashin gwauron zabi musamman abinci da muke amfani da shi, sakamakon rikicin Ukraine da Rasha wadanda suke fitar da kayayyaki.

“Mun ga yadda harkokin kasuwannin duniya ta kasance bayan rufe China da aka yi wanda duk mun san wadannan nan a yanzu su ne suke samar da abubuwa a duniya. Mun ga yadda ake kokarin daidaita bukatuwar abu, kuma wannan dalilin ne ya haifar da tsadar kayayyaki.

“Mun kuma ga yadda aka rasa ayyukan yi a duniya don wasu sun zabi su yi aiki daga gida. Dukkanin wadannan abubuwa su ne suka haifar da kuncin rayuwa a duniya. Za ka iya zuwa Burtaniya da Amurka a baya can babu kuncin rayuwa, amma a yanzu sun shiga ciki.

“A yanzu a Burtaniya suna da kashi 6 cikin 100, a yayin da Turai ake da kashi 9 cikin 100. Idan kuwa aka je Argentina alal misali, suna da kuncin rayuwa sama da kashi 70 cikin 100. Amma idan muka duba a Nijeriya idan muka kwatanta da sauran duniya za mu iya cewa muna da kashi 17 cikin 100 ne kawai.

A lokacin da yake sharhi kan kuncin rayuwar da Nijeriya ke ciki a halin yanzu, kwararren mai sharhin al’amuran yau da kullum a FDTM, Lukman Otunga ya bayyana cewa akwai lokacin da Nijeriya ta yi shiru a kan shiga wani kuncin rayuwa da aka yi.

Ya ce, “A daidai lokacin da wasu kasashe a duniya suke kokarin duba farashin kayayyaki, kasar da ta fi kowacce kasa girman tattalin arziki a Afrika kuma take da masaniyar yadda za ta sassauta kuncin rayuwa. Wannan dabara ce da CBN ya gaza sauya shi wajen inganta tattalin arzikin kasa da habaka shi.

“A yanzu kuncin rayuwa a Nijeriya ya karu sosai a watanni hudu a jere zuwa kashi 17.71 cikin 100 a watan Mayu.

Wanda za a iya cewa shi ne mafi muni tun daga watan Yunin bara, hakan ya sanya aka sami karin farashin abinci da farashin man dizil da kuma karancin dalar Amurka.

Wannan kuma shi ne yadda kayayyaki suke kara tashi a duniya da shirye-shiryen zabe wadanda su ne abubuwan da suke kara tsananin matsalolin da ake fuskanta.

Musamman bayan kalaman da hukumar IMF ta yi game da farashin kayayyaki, inda ta ce zai tashi daga tsakanin kashi 18 da kashi 22 cikin 100 a shekarar 2022.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rabi Shehu Sharada: ‘Yan Siyasa Sun Ci Moriyar Ganga, Sun Yada Kwaurenta!

Next Post

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Nasarori Goma Da BRICS Ta Samu A Bana

Related

Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

4 days ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

4 days ago
Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu
Rahotonni

Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

5 days ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

1 week ago
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

2 weeks ago
Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

3 weeks ago
Next Post
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Nasarori Goma Da BRICS Ta Samu A Bana

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Nasarori Goma Da BRICS Ta Samu A Bana

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya NaÉ—a Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya NaÉ—a Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

September 3, 2025
Shettima

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima

September 3, 2025
Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.