ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Talauci Ya Karu A Nijeriya Da Kashi 14 Cikin 100

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Talauci

Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta fitar da wata kididdiga da ta nuna talauci ya karu a Nijeriya da kashi 14 a cikin 100.

Ta bayyana cewa farashin kayayyakin da ake amfani da su tare da nuna cewa an sami hauhawan farashi da kashi 17.81 a watan Mayu idan aka kwatanta da watan Afrilu da aka sami kashi 16.82 a wannan shekarar duk da yake ya ragu ne a kan abun da aka samu a watan Mayun shekarar da ta gabata ta 2021 da aka sami kashi 17.93.

  • Farashin Kalanzir Da Gas Ya Karu Da Kashi 88 A Cikin Shekara Daya – NBS

Talaudci da kuncin rayuwa a cikin kasa na ta karuwa bisa alamu wanda lamarin ba Nijeriya ba ne kawai duk duniya ne. Bankin Duniya daga baya-bayan nan ya haskako karuwar kuncin rayuwa kusan ilahirin kasashen duniya za su fuskanci wannan matsalar.

ADVERTISEMENT

Bankin Duniya ya bayyana cewa habakar tattalin arziki ya yi kasa da kashi 2.9 cikin dari daga kashi 5.7 cikin dari da aka hassaso a shekarar 2022. Shugaban Bankin Duniya, Dabid Malpass ya yi gargadin cewa yakin Ukraine da annobar Korona da ya janyo rufe China waDanda suka janyo tashin farashin abinci da sauran kayayyakin bukatun yau da kullum su suka shafi tattalin arziki.

Idan aka duba kyau za a ga cewa kuncin rayuwa ba Nijeriya ne kadai ba, ko’ina ne a duniya, akwai kasashe sama da 25 a duniya da suke da kuncin rayuwa. Alal misali Turkiyyya tana da kuncin rayuwa da kashi 73.5 cikin 100, a yayin da yaki ya kara kuncin rayuwa a Sudan ya karu da kashi 192.2 cikin 100.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Rasha da Ukraine kuncin rayuwa ya karu da kashi 18 da 17 cikin 100, idan aka dawo nan Afrika kuwa, Ethiopia yana da kuncin rayuwa ya kai kashi 37.7 cikin 100. Ghana da Angola da Sierra Leone sun kai kashi 27.6 da 23.42 da 22.44 cikin 100 na kuncin rayuwa.

A lokacin da yake magana kan ci gaba da kuncin rayuwa, Mataimakin Gwamnan babban Bankin Nijeriya a fannin tsarin tattarin arziki, Kingsley Obiora ya ce tattalin arzikin duniya yana tafiya ne cikin wani mawuyacin hali.

Ya ce, “Mun ga yadda farashin kayayyaki suka yi tashin gwauron zabi musamman abinci da muke amfani da shi, sakamakon rikicin Ukraine da Rasha wadanda suke fitar da kayayyaki.

“Mun ga yadda harkokin kasuwannin duniya ta kasance bayan rufe China da aka yi wanda duk mun san wadannan nan a yanzu su ne suke samar da abubuwa a duniya. Mun ga yadda ake kokarin daidaita bukatuwar abu, kuma wannan dalilin ne ya haifar da tsadar kayayyaki.

“Mun kuma ga yadda aka rasa ayyukan yi a duniya don wasu sun zabi su yi aiki daga gida. Dukkanin wadannan abubuwa su ne suka haifar da kuncin rayuwa a duniya. Za ka iya zuwa Burtaniya da Amurka a baya can babu kuncin rayuwa, amma a yanzu sun shiga ciki.

“A yanzu a Burtaniya suna da kashi 6 cikin 100, a yayin da Turai ake da kashi 9 cikin 100. Idan kuwa aka je Argentina alal misali, suna da kuncin rayuwa sama da kashi 70 cikin 100. Amma idan muka duba a Nijeriya idan muka kwatanta da sauran duniya za mu iya cewa muna da kashi 17 cikin 100 ne kawai.

A lokacin da yake sharhi kan kuncin rayuwar da Nijeriya ke ciki a halin yanzu, kwararren mai sharhin al’amuran yau da kullum a FDTM, Lukman Otunga ya bayyana cewa akwai lokacin da Nijeriya ta yi shiru a kan shiga wani kuncin rayuwa da aka yi.

Ya ce, “A daidai lokacin da wasu kasashe a duniya suke kokarin duba farashin kayayyaki, kasar da ta fi kowacce kasa girman tattalin arziki a Afrika kuma take da masaniyar yadda za ta sassauta kuncin rayuwa. Wannan dabara ce da CBN ya gaza sauya shi wajen inganta tattalin arzikin kasa da habaka shi.

“A yanzu kuncin rayuwa a Nijeriya ya karu sosai a watanni hudu a jere zuwa kashi 17.71 cikin 100 a watan Mayu.

Wanda za a iya cewa shi ne mafi muni tun daga watan Yunin bara, hakan ya sanya aka sami karin farashin abinci da farashin man dizil da kuma karancin dalar Amurka.

Wannan kuma shi ne yadda kayayyaki suke kara tashi a duniya da shirye-shiryen zabe wadanda su ne abubuwan da suke kara tsananin matsalolin da ake fuskanta.

Musamman bayan kalaman da hukumar IMF ta yi game da farashin kayayyaki, inda ta ce zai tashi daga tsakanin kashi 18 da kashi 22 cikin 100 a shekarar 2022.

Talauci
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Talauci
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Talauci
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Nasarori Goma Da BRICS Ta Samu A Bana

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Nasarori Goma Da BRICS Ta Samu A Bana

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.