• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Biyan Kudin Fansa, Kasurgumin Dan Bindiga Ya Saki Daliba 4 Na Kwalejin Yauri

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Bayan Biyan Kudin Fansa, Kasurgumin Dan Bindiga Ya Saki Daliba 4 Na Kwalejin Yauri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan karbar makudan kudade a matsayin kudin fansa, wani kasurgumin dan fashin nan mai suna Dogo Daji, ya saki hudu daga cikin dalibai 11 da suka yi garkuwa da su a Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya da ke Yauri, Jihar Kebbi.

An tattaro cewa biyu daga cikin daliban da aka sako sun dawo da jarirai biyu a hannunsu.

  • Yadda Manyan Jam’iyyu Suka Fada Cikin Rikici Bayan Zabe
  • Jerin ‘Yan Wasan Kungiya Daya Da Suka Yi Fada Da Juna

Dogo Daji ya jaddada cewa sai an cika wasu sharuda da gwamnatin Jihar Kebbi kafin a sako sauran ‘yan matan.

Majiyoyi sun kara da cewa dole ne iyaye da sauran masu ruwa da tsaki su samar da kudin fansa a lokacin da gwamnatin Jihar Kebbi ta ki biyan bukatun ‘yan bindigar.

Sai da iyayen daliban sun roki ‘yan Nijeriya da su kawo musu agajin kudi domin ceto ‘ya’yansu daga hannun wadanda suka sace su.

Labarai Masu Nasaba

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

A cikin wata wasika da ta aike wa daukacin ‘yan Nijeriya a watan Janairun 2023, wadda Leadership Hausa ta samu, kungiyar da aka fi sani da “Kwamitin Iyayen dalibai 11 da aka sace na F.G.C Birnin Yauri, Jihar Kebbi, Nijeriya,” ta bukaci taimakon kudi domin tara zunzurutun kudi har Naira miliyan 100 a matsayin kudin fansa da za a biya ‘yan ta’adda.

A cikin wasikar, shugaban kwamitin iyayen, Salim Ka’oje da kuma Mista Daniel Alkali, sun ce ‘ya’yansu mata sun kasance a hannun wadanda suka sace su kusan watanni 20 kawo yanzu.

“…Kuma wadanda suka sace ‘yan matan suna neman Naira miliyan 100 kafin su sako su,” in ji su.

Idan za a iya tunawa, an yi garkuwa da daliban mata 11 ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari makarantarsu a ranar 17 ga watan Yuni 2021.

A watan Nuwamban shekarar da ta gabata ne aka ruwaito cewa wasu daga cikin ‘yan matan sun haihu, yayin da wasu kimanin hudu ke dauke da juna biyu a lokacin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaiDan BindigaGarkuwaKudin FansaKwalejin Yauri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Next Post

An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

Related

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

4 hours ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

2 weeks ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

3 weeks ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2

1 month ago
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

1 month ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

2 months ago
Next Post
An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.