• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kamfanin Humanwell Na Sin Ya Taimaka Wajen Gina MasanaAntar Sarrafa Magunguna A Mali

by Sulaiman and CMG Hausa
3 years ago
Humanwell

Fannin sarrafa magunguna muhimmin bangare ne na bukatun al’ummar kowace kasa, duba da yadda fannin ke taka muhimmiyar rawa wajen biyan bukatun kiwon lafiyar al’umma.

A kasar Mali, wannan fanni ya jima yana fuskantar koma baya, amma a yanzu muna iya cewa hakan ya fara sauyawa, domin kuwa bayan shafe tsawon shekaru ’yan kasar ta Mali na sayen magunguna masu tsada da aka sarrafa a ketare. A yanzu haka ’yan kasar sun fara amfani da magungunan da ake sarrafa a cikin kasar.

  • Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da Ukraine Ta Nuna Yadda Sin Ta Sauke Nauyi Dake Wuyanta

A shekarar 2013 ne dai kamfanin sarrafa magunguna na Humanwell mai helkwata a kasar Sin, da hadin gwiwar asusun samar da ci gaba na Sin da Afirka, suka zuba kudi har yuan miliyan 350, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 50, don gina masana’antar sarrafa magunguna irinta ta farko a birnin Bamako, fadar mulkin kasar ta Mali, masana’antar da aka sanyawa suna “Humanwell Africa Pharmaceutical”.

Masana’antar da aka samar karkashin wannan shiri, ta fara aiki bayan shekaru 2, inda take samar da nau’o’in magunguna daban daban da ake amfani da su a cikin kasar, tare da sayar da wasu a kasashe renon Faransa dake yankin yammacin Afirka.

Wannan muhimmin aiki da ya tabbata, albarkacin shigar kasar Mali shawarar nan ta “ziri daya da hanya daya”, ya haifarwa kasar tarin alherai, ciki har da samun kudaden shiga daga masana’antar, yayin da kamfanin na Humanwell Africa Pharmaceutical, ya samar da guraben ayyukan yi har kusan 200 ga alummun yankin da aka kafa shi, inda suke aiki, tare da samun horo a fannonin lura da masana’anta, da jagorancin ci gabanta.

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ko shakka babu wannan yunkuri na dada tabbatar da burin kasar Sin, na yin tafiya tare da kasashe masu tasowa, ciki har da na nahiyar Afirka, ta yadda za a kai ga gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil adama a fannin kiwon lafiya da wanzar da ci gaba. (Saminu Hassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
Daga Birnin Sin

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Tura Jirgin Ruwan Soja Don Kwashe Jama’ar Ta Dake Sudan

Kasar Sin Ta Tura Jirgin Ruwan Soja Don Kwashe Jama’ar Ta Dake Sudan

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.