• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Legas Ta Sayo Motoci Masu Aiki Da Lantarki

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Legas Ta Sayo Motoci Masu Aiki Da Lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya sayo motoci masu aiki da lantarki, inda ya ce “matakin na nufin mazauna Legas za su daina aiki da man fetur su soma amfani da makamashi mai tsafta.”

Gwamnatin Jihar Legas ta ce ta sayo sabbin motoci masu amfani da larntarki da zummar yin aiki da su a matsayin motocin haya.

  • ‘Yan IPOB 9 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Kashe ‘Yansanda A Imo
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Makamai A Zamfara

Gwamnan Jihar, Babajide Sanwo-olu ne ya bayyana haka a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Lahadi.

Ya ce an sayo motocin ne da zummar saukaka sufuri da kuma sake tasirin sauyin yanayi a Legas, birni mafi girma a Afirka da ke da mutane fiye da miliyan 15.

Wannan ne karon farko da hukumomi a Nijeriya suka sanar da sayo irin wadannan motoci domin yin sufuri.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sanwo-Olu ya ce matakin zai tabbatar da ”tsaftace tsarin sufuri” a jihar.

”Sabbin motocinmu masu aiki da lantarki za su inganta sufuri da kuma rage gurbata muhalli.

Hakan na nufin mazauna jihar za su yi murna da amfani da man fetur sannan su yi maraba da makamashi mai tsafta,” a cewar gwamnan a sanarwar da ya fitar.

Kawo yanzu ba a san adadin motocin da gwamnatin ta saya ba, amma Sanwo-olu ya ce za a karo motoci masu yawa da ke aiki da lantarki don inganta sufuri a jihar

Ya kara da cewa nan da watanni masu zuwa za a soma amfani da motocin a “matakin gwaji.”

A cewarsa hakan zai bai wa gwamnati damar ”tattara isassun bayanai game da aiki da makamashi maras gurbata muhalli” da kuma kwatanta shi da yadda ake sufuri da masu aiki da fetur da zummar inganta tsarin sufuri.

Mutanen jihar sun yi maraba da wanna mataki ko da yake wasu sun nuna dari-dari game da dorewarsa ganin yadda shirye-shirye da dama da gwamnatoci ke bijirowa da su suke lalacewa.

Nijeriya ta yi kaurin suna wurin dauke wutar lantarki don haka mutane ke ganin zai yi wahala matakin ya dore.

Wasu kuma sun bayyana cewa cunkoson ababen hawar da ake fama da shi a Legas zai zama kalubale ga wannan shiri.

Sai dai gwamnati ta ce za ta samar da “tashoshin da za a rika yin cajin motoci masu aiki da lantarkin.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Babajide Sanwo OluBasLantarkiLegasMotoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Samu Yawaitar Tafiye Tafiye Da Tagomashi A Bangaren Yawon Bude Ido Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Na Kwanaki 5 A Kasar Sin

Next Post

Syria: Kasar Sin Tana Taka Muhimmiyar Rawa Da Yin Tasiri A Harkokin Kasa Da Kasa

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

13 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

22 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

23 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Syria: Kasar Sin Tana Taka Muhimmiyar Rawa Da Yin Tasiri A Harkokin Kasa Da Kasa

Syria: Kasar Sin Tana Taka Muhimmiyar Rawa Da Yin Tasiri A Harkokin Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.