• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sudan: Rukuni Na Biyu Na ‘Yan Nijeriya Sun Iso Abuja

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Sudan: Rukuni Na Biyu Na ‘Yan Nijeriya Sun Iso Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kashi na biyu na mutanen da aka kwashe sun kunshi ‘yan Nijeriya 130; mata 128 da maza biyu sun isa Abuja ta jirgin saman Tarco.

Da misalin karfe 4 na yamma wadanda aka kwaso suka isa filin jirgin.

  • Qin Gang Ya Halarci Taron Ministocin Wajen Kasashen Kungiyar SCO
  • Bukatar Tafiyar Da Tattalin Arzikin Nijeriya A Dunkule Ta Hanyar Rage Amfani Da Tsabar Kudi

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da babban daraktan hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), Mustapha Ahmed ya ce tuni wasu karin ‘yan Nijeriya 800 ke kan hanyarsu ta zuwa filin jirgin na Masar domin kwaso su zuwa Nijeriya.

Shugaban NEMA, wanda ya tarbi wadanda aka kwaso daga Sudan, ya ce Max Air mai daukar fasinjoji 560 da kuma Azman Air mai daukar fasinjoji 400 tuni suka isa kasar Masar domin jigilarsu.

Ya kuma ce an kulla alaka da jirgin Air Peace da gwamnatin tarayya za ta yi duk mai yiwuwa don kwaso dukkan ‘yan Nijeriya daga Sudan.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Wasu daga cikin wadanda aka kwaso, wadanda suka zanta da LEADERSHIP, sun ce abin ya yi muni matuka, amma sun ji dadin dawowarsu gida.

Daya daga cikinsu wata Hajia Medina ta ce ta yi balaguro zuwa tashar jiragen ruwa na Sudan da kan iyakar Masar cikin mawuyacin hali.

Sai dai ta yaba wa gwamnatin tarayya da ta kawo musu dauki.

Har ila yau, shugaban kafafen yada labarai na NEMA, Ezekiel Manzo ya ce, “Bugu da kari, bisa la’akari da muhimman bukatun al’ummar Nijeriya da ke kan iyakar Masar, NEMA ta ci gaba da samar musu da abinci da ruwa da sauran muhimman kayayyaki a yayin da suke jiran izinin shiga kasar Masar don jigilar su zuwa Najeriya.

“NEMA da Ofishin Jakadancin Nijeriya a Masar ne suka samar da abincin.

“Ta hanyar shigar da wasu kamfanonin jiragen sama, za a kara kaimi wajen kwashe su, haka zalika, Taco aviation da ke Sudan ta himmatu wajen inganta jigilar ‘yan kasarmu zuwa gida daga gabar tashar jiragen ruwan Sudan.

“Babban daraktan NEMA, ya yaba da amincewar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba hukumar; domin gudanar da aikin kwaso mutanen.

“Haka zalika, babban daraktan hukumar NEMA ya yaba da irin tallafin da ministar kula da jin kai da agaji da ci gaban al’umma, Hajiya Sadiya Umar Farouq ta bayar.

Ya kuma umarci masu ruwa da tsaki da su ci gaba da hada kai da hukumar NEMA domin tabbatar da cewa an kammala kwaso ‘yan Nijeriya baki daya”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan NijeriyaMasarNEMASudan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Qin Gang Ya Halarci Taron Ministocin Wajen Kasashen Kungiyar SCO

Next Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Al’ummar Afirka Ne Ke Da Ikon Tsokaci Kan Hadin-Gwiwar Su Da Kasar Sin

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

10 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

15 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

16 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

1 day ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Al’ummar Afirka Ne Ke Da Ikon Tsokaci Kan Hadin-Gwiwar Su Da Kasar Sin

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Al’ummar Afirka Ne Ke Da Ikon Tsokaci Kan Hadin-Gwiwar Su Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Sudan

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.