• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahara Sun Kai Hari Ofishin ‘Yan Sanda A Kogi

by Sadiq
3 years ago
Ofishin 'Yan Sanda

Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ba sun kai hari ofishin ‘yan sanda da ke Eika-Ohizenyi a karamar hukumar Okehi a Jihar Kogi, inda suka kashe wani jami’in dan sanda mai suna Mista Jibril, wanda aka fi sani da ‘Yellow’.

Wani mazaunin yankun mai suna Mallam Momoh Abubakar, ya tabbatar wa da wakilinmu cewar, ‘yan bindigar sun kai harin da misalin karfe 12:15 ma dare, inda suka jefa wani abu mai fashewa ofishin, lamarin da ya sanya daukacin al’ummar yankin tashi daga bacci.

  • Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya
  • Macizai Da Kunamu Na Barazana Ga Rayukan Mutanen Da Aka Sace A Harin Jirgin Kasa

Ya kara da cewa ‘yan bindigar sun dauki tsawon awa biyu suna sha’aninsu a yankin ba tare da an samu dauki daga jami’an tsaro ba.

Sannan ya ce jami’in dan sanda guda daya da ke aiki a lokacin ya rasa ransa, yayin da kuma suka cinna wa motar aikin ‘yan sandan wuta.

“Ina son amfani da wannan dama don jan hankalin jami’an tsaro da su zage damtse wajen dakile irin wannan hari da aka shafe awa biyu ba tare da kawo dauki ba.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

“Harin farko da aka kai ofishin ‘yan sandan ranar Juma’a ne shekaru biyar da suka wuce, wannan ma kuma ranar Juma’a aka yi kuma abun mamaki babu wanda aka cafke da ke da alaka da harin.

“A yanzu dana ke magana da kai, akwai firgici da tashin hankali a zukatan mutane. Muna rokon gwamnati ta kawo dauki saboda wannan yanki ba zai iya jurar hare-haren da ake kawo ba, in ji Abubakar.

A halin da ake ciki an ajiye gawar dan sandan da aka kashe a babban asibitin Obandege.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mista Edward Ebuka, ya tabbatar da faruwar harin.

Sai dai ya ce wanda suka kai harin ba zasu tsira ba, domin rundunar ‘yan sandan jihar zata bankado inda suka shiga.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 
Labarai

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Next Post
Kotun Daukaka Kara Ta Yi Watsi Da Karar Buhari Kan Sashe Na 84(12) Na Dokar Zabe

Kotun Daukaka Kara Ta Yi Watsi Da Karar Buhari Kan Sashe Na 84(12) Na Dokar Zabe

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.