ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Macizai Da Kunamu Na Barazana Ga Rayukan Mutanen Da Aka Sace A Harin Jirgin Kasa

by Khalid Idris Doya
4 years ago
kaduna

Sama da kwanaki tamanin da kai hari da yin garkuwa ga fasinjojin jirgin kasa a Kaduna, sama da mutum 50 da suka hada da mata, yara, manya da kananan har yanzu su na hannun ‘yan garkuwa da mutanen cikin mayuwacin hali da kuncin rayuwa.

Bayanai da suke fitowa na nuna da cewa tabbas halin da fasinjojin ke ciki ya munana don kuwa macizai da kunamu suna kai musu farmakin inda zuwa yanzu aka samu rahoton cewa mutum 9 daga cikinsu sun mutu sakamakon wannan saran da macizai da kunamai suke musu.

  • Harin Jirgin Kasa: Ana Zargin Macizai da Kunamu Sun Kashe 9 Cikin Mutanen da Aka Sace

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin mai bai wa Sheikh Ahmad Gumi shawarwari a bangaren yada labarai, Malam Tukur Mamu, wadda ya shiga tsakani aka samu nasarar sako mutum 11 daga hannun masu garkuwan.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, wannan lamarin na faruwa ne sakamakon dajin da masu garkuwan suka ajiye fasinjojin na fuskantar ruwan sama don haka macizai kan fito daga cikin ramuka don sauya wajen zama a irin wannan yanayin ne suka haduwa da mutanen tare da sararsu.

Rahoton ya kuma yi zargin cewa, ana fargabar sama da mutum 9 daga cikin fasinjojin sun mutu a sakamakon wannan mummunar yanayin da suke ciki a yanzu haka.

LABARAI MASU NASABA

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

A cewar Mamu, mafiya yawa daga cikin fasinjojin zai yi matukar wuya su iya cigaba da rayuwa idan aka shafe wasu karin makonni a hannun masu garkuwan lura da yanayin halin lafiyarsu da ya tabarbare ba tare da kuma samun kulawar maganin da suka dace ba a cikin dajin.

Har-ila-yau, ya ce akwai bukatar gwamnati da masu ruwa da tsaki kan lamarin su kara azama domin ganin an cetosu da ransu daga hannun ‘yan garkuwan.

LEADERSHIP HAUSA ta labarto cewa, ‘yan ta’addan sun kai hari ga jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja ne a ranar 28 ga watan Maris din 2022 tare da kashe mutum 9 hadi da yin garkuwa da a kalla mutum 63 da suke cikin jirgin ciki hard a manajan gudanarwa na bankin BOA, wanda aka sakeshi bayan zargin ahlinsa sun biya miliyan 100 na diyyarsa.

Mamu, wanda mawallafin jaridar ‘Desert Herald’ ne, ya ce, tuni ya sanar da shugabannin Nijeriya, jami’an tsaro, da masu ruwa da tsaki kan halin da ake ciki domin daukan matakan da suka dace na gaggauta ceto fasinjojin lura da hadin kunci da suke ciki.

“Yanzu ba lokacin batutuwan da suka shafi siyasa ba ne, rayukan mutane na da matukar muhimmanci, raunanan ‘yan Nijeriya na daga cikin wadanda wannan lamarin ya shafa. Yanayin lafiyarsu na kara lalacewa kullum.

Hatta dabbobi da wuya su iya rayuwa a muhallin da ake kuntata musu da tilasta musu, balle mutanen da suka doshi kusan wata uku zuwa yanzu.

“Na yi imanin gwamnati tana sane da ko ta samu bayanai daga mutum 11 da suka kubuta daga cikin wadanda lamarin ya shafa. Abun damuwa ne gare ni idan na ga lamari irin wannan an kasa daukan matakan da suka dace a kai, wanda kuma lallai na bukatar a gaggauta maida hankali sosai wajen yin abun da ya kamata.”

Ya jawo hankalin gwamnati da ta yi amfani da hanyoyi na hikima da diflomasiyya wajen shawo kan matsalolin tare da ceto wadanda suke tsare gami da sauran batutuwan da suka shafi matsalar tsaro fiye da batun zaben 2023.

Sai dai kuma, Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya ce ya umarci jami’an tsaro su tabbatar da sun ceto mutanen da ransu tare da sada su da iyalansu.

Mai magana da yawun shugaban kasan, Malam Garba Shehu ya sanar da umarnin na Shugaba Buhari a ranar Talata inda ya kara da cewa gwamnati tana ci gaba da bitar batun wadanda aka sacen kuma ana ci gaba da dukkan kokarin ganin an ceto ragowar da suka rage a hannun ‘yan ta’addan su 51.

Ya kara da cewa, umarnin da Buhari ya bayar baro-baro a fili shi ne a ceto fasinjojin da suka rage da ransu zuwa gida, kuma jami’an tsaro suna sane da aikin da ya rataya a wuyansu kuma sun dukufa wajen aiki da cikawa sakamakon umarnin da shugaban ya bayar.

Iyalan Wadanda Aka Yi Garkuwa Da Su Sun Bayyana Yadda Aka Yi Watsi Da Su
Kazalika, wasu daga cikin iyalan fasinjojin da aka yi garkuwa da su, sun ce, bai dace a dawo jigilar fasinjoji ba har sai an ceto dukkanin fasinjojin da suke hannun masu garkuwa, suna masu cewa akwai kuma bukatar daukan tsauraran matakan kare rayukan da lafiyan fasinjoji kafin dawo da jigilar.

Wadanda suke magana ta bakin kakakinsu, Dakta Abdulfatai Jimoh, iyalan sun zargi hukumar kula da sufurin jiragen kasa a Nijeriya (NRC) da kin mutunta umarnin shugaban kasa Muhammadu Buhari na zama tare da su da yin hulda a kai a kai don cimma nasarar ceto wadanda suke tsare.

Jimoh ya kara da cewa, “Mun ji dadi bisa kokarin da gwamnati ta fara yi na tattaunawa da masu garkuwa da ‘yan uwanmu,” ya kuma yi kira ga gwamnatin da ta hanzarta wajen cimma matsaya da masu garkuwan domin makusantan nasu su samu kubuta.

Ya ce, suna kewar ‘yan uwansu tun lokacin da aka sacesu, sai ya gargadi hukumar NRC daga shirinta na dawo da jigilar fasinoji, ya ce muddin ba a samar da wadaccen tsaro ba, babu amfanin dawo da sufurin.

Sai dai kuma Kakakin hukumar NRC, Mahmood Yakub, ya karyata labaran da aka yada na cewa suna shirin dawo da jigilar jirgin kasan a wannan layin dogon da ake batu a kai.

Yakub ya kara da cewa, “Muna yin duk mai yiyuwa domin tabbatar da ceto wadanda suke tsare. Lallai muna kan kokari sosai, mun kuma tattauna da shugaban iyalan wadanda lamarin ya shafa.

“Muna aiki sosai domin ganin dukkanin wadanda aka sace sun fito cikin koshin lafiya. Muna kan kokarin sosai.”

Macizai
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Birnin Legas Ya Zama Na Biyu Mafi Muni Wajen Yin Rayuwa A Duniya

Birnin Legas Ya Zama Na Biyu Mafi Muni Wajen Yin Rayuwa A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.