• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 10 Sun Mutu Bayan Shan Shayin Gadagi A Wajen Daurin Aure A Kano

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Mutum 10 Sun Mutu Bayan Shan Shayin Gadagi A Wajen Daurin Aure A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutane 10 ne aka ruwaito cewa sun mutu, inda wasu kuma da dama, aka kwantar da su a asibiti bayan da suka sha shayin gadagi wanda ake zargin an hada shi ne da wani ganyen shayin Zakami.

Mutanen sun sha shayin ne, a taron wani biki a Jihar Kano.

  • Buhari Ya Nada Sabon Mai Ba Da Shawara Kan Sha’anin Tsaro
  • Ma’aikatan Filato Sun Fara Yajin Aiki Kan Rashin Biyan Su Albashi

Zakami dai, na dauke da wani sanadarin da ke sanya wa wanda ya sha kuzari.

Lamarin ya auku ne a ranar Talata a unguwar Sheka da ke a karamar hukumar Kumbotso a Jihar Kano.

Daya daga cikin ganau, Sanusi Yahaya wanda kuma babban yaya ne ga amaryar da aka daura wa auren, ya bayyana cewa, ana zargin ana hada shayin da kwaya da kuma ganyen Zakamin.

Labarai Masu Nasaba

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Ya ce, abin kusan ya zama jiki, musamman ga masu ta’ammali da kayan maye da ke yin amfani da shi a lokacin bukukuwa.

A cewarsa, suna dafa shayin kuma ba su san adadin kwayar da ke cikin shayin ba, inda hakan ya sa wasu suka yi watsi da shayin wasu kuma suka matsa sai sun sha shayin bisa cewarsu kwakwalwarsu za ta iya dauka.

Ya ci gaba da cewa, bayan sun sha shayin ne, sai mutum biyu suka fara mutuwa, wasu kuma suka farfado, inda kuma garzaya da wasu asibiti.

Shi ma wani ganau, Abdullahi Muhammad, ya bayyana cewa, a ranar Talata mutum bakwai sun mutu, inda aka danganta mutuwar da shan shayin.

A cewarsa, ba mu san yawan adadin wadanda suka mutu ba, amma da safiyar Talatar an tabbatar da mutuwar mutane bakwai, inda ya ce, wasun ma ba wanda ya gayyace su zuwa daurin auren sun zo ne kawai don su fake da daurin, don su sha kayan maye.

Ba a dai iya jin ta bakin angon ba, don jin ta nasa bangaren kan lamarin.

Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yansandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa, rundunar da kuma caji ofis na yankin da lamarin ya auku, ba su samu rahoton faruwar lamarin ba.

Amma ya yi alkwarin yin karin haske da zarar ya samu rahoton faruwar lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Daurin AureGadagikanoShayiShekaZakami
ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Nada Sabon Mai Ba Shi Shawara Kan Sha’anin Tsaro

Next Post

Za A Tafka Mamakon Ruwan Sama A Arewa A Kwanaki Masu Zuwa —NiMet

Related

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

59 minutes ago
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL
Manyan Labarai

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

3 hours ago
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

4 hours ago
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi
Labarai

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

5 hours ago
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya
Labarai

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

6 hours ago
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana
Labarai

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

14 hours ago
Next Post
Za A Tafka Mamakon Ruwan Sama A Arewa A Kwanaki Masu Zuwa —NiMet

Za A Tafka Mamakon Ruwan Sama A Arewa A Kwanaki Masu Zuwa —NiMet

LABARAI MASU NASABA

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.