• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

by Bushira Nakura
2 years ago
in Adon Gari
0
Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

As a prelude to the celebration of International Women's Day, the Central African Minister of Social Action and Family, Ms. Gisel PANA, visited the women in Bimbo Women's Prison and Corrections. On occasion, women prisoners have exhibited for sale works produced as part of Income Generating Activities, with the support of MINUSCA. An action aimed at contributing to their reintegration.www.icj-cij.org

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Madam Amina J. Mohammed ita ce mataimakiyar Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya kuma shugabar kungiyar ci gaba mai dorewa ta Majalisar Dinkin Duniya.

Idan za a tunawa Amina Mohammed ta rike Minista a gwamnatin Muhammadu Buhari kafin ta zama mataimakiyar sakatariyar majalisar UN a 2017.

  • Yadda Likita Ya Yi Lalata Da Wata Mai Jinya A Asibitinsa A Jihar Kwara
  • Manyan Jami’an Kasashen Sin Da Amurka Sun Tattauna Game Da Alakar Kasashen Biyu

Kafin nadin nata, Ms. Mohammed ta kasance ministar muhalli ta Tarayyar Nijeriya inda ta jagoranci kokarin kasar kan ayyukan sauyin yanayi da kokarin kare muhalli.

Ms. Mohammed ta fara shiga Majalisar Dinkin Duniya ne a shekarar 2012 a matsayin mai baiwa Ban Ki-moon tsohon babban sakataren Manofofin Ci Gaban Karni Na Majalisar Dinki Duniya (MDD) shawara Ta musamman da alhakin tsare-tsaren ci gaba bayan 2015.

Ta jagoranci tsarin da ya haifar da yarjejeniyar duniya ta shirin cigaba mai dorewa Nan da 2030.

Labarai Masu Nasaba

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Ms. Mohammed ta fara aikinta ne da aikin zayyana makarantu da asibitoci a Nijeriya. Ta yi aiki a matsayin mai ba da shawara ta mayar da hankali kan inganta ilimi da sauran ayyukan zamantakewa, kafin ta shiga cikin ma’aikatun gwamnati, inda ta kai matsayin mai ba da shawara ga shugabannin hudu da suka biyo baya a kan talauci, gyara sassan gwamnati, da ci gaba mai dorewa.

An bai wa Ms. Mohammed digirin girmamawa da dama, kuma ta yi aiki a matsayin mataimakiyar farfesa, inda ta yi lacca kan ci gaban kasa da kasa. Wadda ta samu lambobin yabo daban-daban na duniya, Ms. Mohammed ta yi aiki a manyan kwamitocin ba da shawarwari na kasa da kasa. Tana da ‘ya’ya shida kuma tana da jikoki hudu.

MADOGARA (UN ORGANIZATION)

Haihuwa

An haifi Amina Jane Mohammed a Birnin Liberpool, dake Ingila a ranar 27 ga watan Yunin, 1961 mahaifinta likitan dabbobi ne  da kuma mahaifiyarta malamar Jinya ce (nurse) Asalin ta Bafulatana ce  daga Jihar Gombe Nijeriya.

Karatu

Amina ta halarci makarantar firamare a Kaduna da birnin Maiduguri a Nijeriya, sai kumaMakarantar “The Buchan School” da ke tsibirin Isle of Man.

Daga bisani ta halarci kwalejin Henley Management College dake birnin London a 1989. Bayan ta kammala karatun ta ne mahaifinta ya nemi ta da ta dawo gida Nijeriya.

Ayyuka

A tsakanin shekarun 1981 zuwa 1991, Amina tayi aiki da “Archcon Nigeria”, wani kamfanin zane-zane da suke da alaka da kamfanin zane-zane na Norman and Dawbarn da ke Ingila A 1991, ta samar da kamfanin Afri-Projects Consortium, sannan daga 1991 zuwa 2001 itace darekta mai zartarwa na kamfanin.

Daga shekara ta 2002 har zuwa shekara ta 2005, Amina ta shirya wani gangami da ilimantarwa game da jinsi karkashin United Nations Millennium Project. (Manufar manufar ita ce rage talauci, yunwa, cututtuka, jahilci, gurbacewar muhalli, da kuma cin zarafi tsakanin jinsi)

Amina ta rike matsayin mataimakiya ta musamman (Senior Special Assistant) na shugaban kasa akan shirin Millennium Debelopment Goals, Manofofin Cigaban Karni Na Majalisar Dinki Duniya (MDGs). A cikin shekara ta 2005, an zarge ta da amfani da kudin tallafi na kasa a wajen ayyukan MDGs.

Amina ta kasance wacce ta kafa kuma ta samar da kamfanin Center for Debelopment Policy Solution, sannan kuma a matsayin farfesa ta daliban masters a jami’ar Columbia.

A tsakanin wannan lokaci, tayi aiki a matsayin mai bada shawarwari na kungiyoyi daban daban na duniya wanda ya hada da, babban sakatariya a Majalisar Dinkin Duniya (UN) don zama na musamman akan Post-2015 “Debelopment Agenda”; da kuma Independent Edpert Adbisory Group.

Sannan har wayau ta rike matsayin chairman a Hukumar Ilimi, Kimiyya da Al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya United Nations Educational, Scientific and Cultural Organization (UNESCO), da sashin bincike da bayanai akan ilimi na duniya “Global Monitoring Report on Education” (GME).

Har zuwa shekara ta 2012, Amina tana daya daga cikin muhimman mutane a taron e Post-2015 Debelopment Agenda, (Ajandar ci gaban bayan 2015 wani tsari ne daga 2012 zuwa 2015 wanda Majalisar Dinkin Duniya ke jagoranta don ayyana tsarin ci gaban duniya nan gaba wanda zai cimma nasarar muradun karni, Sabon tsarin, wanda ya fara daga 2016 ana kiransa Manufofin Ci Gaban Dorewa). inda take aiki a matsayin mai bada shawara na musamman ga shugaban majalisar dinkin duniya watau Ban Ki-moon, sannan tana daga cikin mutane na musamman na “High Lebel Panel of Eminent Persons (HLP)” da majalisar Open Working Group (OWG) da dai sauransu.

Daga shekara ta 2014, tayi aiki a matsayin babban sakatariya na “independent Edpert Adbisory Group on the Data Rebolution for Sustainable Debelopment.

Ministan Muhalli (2015-2017)

Amina tayi aiki a matsayin ministan muhalli a karkashin mulkin shugaba Muhammadu Buhari daga watan Nuwamaban shekara ta 2015 zuwa watan Febrerun shekara ta 2017. A wannan lokaci itace wakiliyar Nijeriya a Kungiyar Kasashen Nahiyar Afurka wato “African Union (AU)” fannin kawo canji wanda Paul Kagame ke jagoranta.

Ta ajiye aikin Ministan muhalli a ranar 24 ga watan Febrerun 2017.

A cikin shekara ta 2017, wata kungiya mai zaman kanta ta zargi Amina da cewa tana ba da izini ga kamfanonin kasar China wajen diban itace timber zuwa kasashensu ba tare da izinin gwamnatin tarayya ba, a lokacin tana ministan muhalli na Nijeriya.

Amma daga bisani gwamnatin Nijeriya ta karyata zargin.

Mun samo daga Turakar Saliadeen a Dandalin Is’haki Idris Guibi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Amina MuhammadTarihi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci

Next Post

Xi Ya Yi Kira Da A Mayar Da Yankin Biranen Beijing Da Tianjin Da Hebei Mafarin Neman Zamanantar Da Kasar Sin

Related

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

1 month ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

2 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

5 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

5 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

6 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

7 months ago
Next Post
Xi Ya Yi Kira Da A Mayar Da Yankin Biranen Beijing Da Tianjin Da Hebei Mafarin Neman Zamanantar Da Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Mayar Da Yankin Biranen Beijing Da Tianjin Da Hebei Mafarin Neman Zamanantar Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

July 1, 2025
Uwargidan Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma

Uwargidan Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma

July 1, 2025
Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

July 1, 2025
Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci

Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci

July 1, 2025
Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 

Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 

July 1, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

July 1, 2025
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

July 1, 2025
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

July 1, 2025
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.