• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barawo Ne Ke Yin Ihun Kama Barawo

by CMG Hausa
2 years ago
barawo

Sakatariyar harkokin kudi ta kasar Amurka Janet Yellen ta halarci taron ministocin kudi da shugabannin manyan bankuna na kasashen kungiyar G7 a kwanan baya, inda ta yi kira da a dauki “matakai na bai daya”, don tinkarar abin da take kira wai “matakan tattalin arziki da kasar Sin ta dauka don tilasta wasu”. Lallai barawo ne ke yin ihun kama barawo ke nan, sakamakon yadda hakikanin al’amuran da suka faru suka shaida ainihin wadda ke daukar irin wadannan matakai.

In an tabo maganar “tilastawa” a huldar kasa da kasa, to za a gano cewa, Amurka da kanta ce ta kirkiro wannan ra’ayi tare da aiwatar da shi a kullum. In ba a manta ba, a shekarar 1971, Alexander George, shehun malami a jami’ar Stanford ya gabatar da ra’ayin nan na “matakan diplomasiyya don tilasta wasu”, don yin bayani a kan manufar kasar Amurka a kan kasashen Laos da Cuba da kuma Vietnam. Kasar Sin a nata bangaren, har kullum tana sa kaimi ga kasa da kasa da su bude kofarsu ta fannin tattalin arziki, kuma tana tsayawa tsayin daka a kan kin yarda da daukar matakan tattalin arziki don tilasta wasu.

  • Xi Ya Gana Da Shugaban Eritrea

A ganin kasar Amurka, moriya ce kawai za ta dore a maimakon zumunta. Don haka ma, ko kawayenta ma ba su tsira daga matakanta na tilas ba. In mun duba tarihi, kamfanin Toshiba na Japan da Siemens na Jamus da kuma Alstom na Faransa, wadanda dukkaninsu kamfanoni ne na kasashe kawayen kasar Amurka, duk sun fuskanci irin matakan da Amurka ta dauka, sakamakon yadda suka zama kalubale gare ta.

Nan ba da jimawa ba, za a fara taron kolin G7, kuma da yawa daga cikin kasashen rukunin sun taba yin hasara sakamakon matakan tattalin arziki da Amurka ta dauka don tilasta su, wadanda ya kamata su yi tunani sosai a kan abin da ya faru gare su, idan dai Amurka ta kare aniyarta ta sanya batun “tinkarar matakan tattalin arziki don tilasta wasu” cikin ajandar taron.(Lubabatu)

 

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
Daga Birnin Sin

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
Next Post
Sin: Ya Kamata G7 Ta Bukaci Amurka Ta Daina Yunkurin Raba Duniya Gida 2

Sin: Ya Kamata G7 Ta Bukaci Amurka Ta Daina Yunkurin Raba Duniya Gida 2

LABARAI MASU NASABA

Maganin Nankarwa (4)

Maganin Nankarwa (4)

November 8, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.