ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

…Manyan Kalubalen Da Sabbin Shugabannin Majalisa Za Su Iya Fuskanta

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Majalisa

Masu sharhin al’amurar siyasa suna ganin akwai jan aiki a gaban shugabannin majalisar dokakin Nijeriya ta 10 wadanda suka hada da samun goyon bayan dukkan ‘yan majalsa.

Sanin kowane akwai rarrabuwar kai a majalisun dokokin Nijeriya, musamman a daidai lokacin da aka fafata zabe wasu suka yi nasara, yayin da wasu suka yi rashin nasara.

  • Yariman Bakura Ya Taya Akpabio Murnar Zama Shugaban Majalisar Dattawa Ta 10
  • Sin: Bai Kamata A Shigar Da Salon Fito-na-fito Cikin Tsarin Ayyukan Hukumomin Hada-hadar Kudi Na Kasa Da Kasa Ba

Masu sharhin suna ganin zai yi wahala ‘yan majalisar da suka fadi su amince da sabbin shugabannin, saboda tun lokacin da jam’iyyar APC da Shugaban kasa Tinubu suna fito karara suka bayyana ‘yan takarar da suke bukatan zama shugabanin majalisar dokokin Nijeriya aka samu baraka da sauran ‘ya’yan jam’iyya da ma ‘yan dawa, inda suke ganin ana kokarin katsalandan a sha’anin shugabancin majalisa.

ADVERTISEMENT

Masana suna ganin cewa idan har dan takarar da shugaban kasa yake so suka samu nasara, to majalisar za ta kasance ‘yan amshin shata, wato duk kudurin shugaban kasa za a aiwatar masa da shi ba tare da samun turjiya ba.

Amma kuma wasu na ganin duk da cewa ‘yan takarar shugaban kasa ne suka yi nasara, shugaban kasa yana iya samun turjiya a kan kudurinsa, domin kuwa sai an samu amincewa daga sauran ‘yan majalisa kafin a amince da kudurin da shugaban kasa ya bijiro da shi.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Da yake amsa tambayoyin manema labarai a fadar shugaban kasa jim kadan bayan sabbin shugabannin majalisar sun gana da shugaban kasa, Shugaban Majalisar Wakilai, Hon. Abbas Tajuddeen ya jaddada cewa ba za su zama ‘yan koron bangaren zartaswa ba, “ba ‘yan amshin shata za mu zama ba, duk abin da bangaren zartaswa ya aiko za mu yi masa duba na tsakanaki domin tabbatar da cewa ya dace da kudirin kawo wa al’umma ci gaba.”

Sai dai kuma, a duk lokacin da aka samu sabbin shugabanni na majalisa, sukan fadi haka amma daga baya aikinsu ya saba da abin da suka fada. Shi ya sa yanzu ‘Yan Nijeriya za su zuba na mujiya su gani, ‘yan amshin shata aka zaba ko masu kishin kasa? Lokaci ne kadai zai tabbatar da haka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace
Rahotonni

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
Tinubu Ya Nuna Kwarewa Da Gogewa A Sha’anin Mulkin Nijeriya – Bishir Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Nuna Kwarewa Da Gogewa A Sha’anin Mulkin Nijeriya – Bishir Dauda

December 19, 2025
Next Post
NIS Reshen Ribas Ta Bukaci Mutunta Umarnin Bangaren Zartarwa Kan Aikin Yi Ga ‘Yan Kasa

NIS Reshen Ribas Ta Bukaci Mutunta Umarnin Bangaren Zartarwa Kan Aikin Yi Ga ‘Yan Kasa

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.