• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Duminsa: Tinubu Ya Kori Hafsoshin Tsaron Nijeriya, Ya Nada Sabbi

Ya nada Ribadu a matsayin babban mai ba shi shawara kan sha'anin tsaro (NSA)

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Da Dumi-Duminsa: Tinubu Ya Kori Hafsoshin Tsaron Nijeriya, Ya Nada Sabbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya amince da yi wa dukkan shugabannin hafsoshin tsaron Nijeriya da sufeto-Janar na ‘yan sanda da masu ba da shawara kan sha’anin tsaro da Kwanturola-Janar na Hukumar Kwastam murabus daga Ma’aikatunsu tare da maye gurbinsu nan take.

Hafsan hafsoshin sun hada da babban hafsan tsaro, Lucky Irabor da babban hafsan soji, Farouk Yahaya da Shugaban Hafsan Sojin Ruwa, Awwal Gambo sai shugaban hafsan sojin sama, Isiaka Amao da kuma Sufeto Janar na ‘Yansanda, Usman Alkali.

  • Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa
  • Yanzu-yanzu: Tinubu Na Ganawa Ta Farko Da Shugabannin Tsaro

A cewar sanarwar da ta fito daga ofishin sakataren gwamnatin tarayya, sabbin jami’an da aka nada sune:
Mallam Nuhu Ribadu a matsayin babban mai ba da shawara kan sha’anin tsaron Nijeriya.

Sauran sun hada da “Maj. Janar C.G Musa Shugaban Hafsan Tsaro, Maj. T. A Lagbaja

“Shugaban hafson sojojin ruwa, Rear Admirral E. A Ogalla

Labarai Masu Nasaba

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

“AVM H.B Abubakar Shugaban Hafsan Sojan Sama sai DIG Kayode Egbetokun Mukaddashin Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda.

“Maj. Janar EPA Undiandeye, matsayin shugaban hukumar leken asiri na kasa

Shugaban ya kuma amince da nadin:

“Col. Adebisi Onasanya, a matsayin kwamandan rundunar Soji.

“Lt. Col. Moshood Abiodun Yusuf, matsayin shugaban runduna ta 7, Asokoro, Abuja

“Lt. Col. Auwalu Baba Inuwa, matsayin shugaban runduna ta
177, Keffi, Nasarawa State

“Lt. Col. Mohammed J. Abdulkarim, matsayin shugaban runduna ta 102, Suleja, Niger

“Lt. Col. Olumide A. Akingbesote, matsayin shugaban runduna ta 176, Gwagwalada, Abuja

Kazalika, shugaban ya amince da nadin wasu hafsoshin soji a fadar shugaban kasa da suka hada da Maj. Isa Farouk Audu (N/14695) Babban Jami’i mai kula da Makamai na Gidan Gwamnati

“Capt. Kazeem Olalekan Sunmonu (N/16183) Babban Kwamandan Na Biyu

“Maj. Kamaru Koyejo Hamzat (N/14656) Babban Kwamandan Hukumar Leken Asiri ta Soja na fadar gwamnati

“Maj. TS Adeola (N/12860) Kwamanda, Makamai na Gidan Gwamnati

“Lt. A. Aminu (N/18578) Kwamandan Makamai na Gidan Gwamnati

Shugaban ya kuma amince da nadin wasu karin masu ba da shawara na musamman guda biyu (2), da manyan mataimaka biyu (2), wato:

“Hadiza Bala Usman mai ba da shawara ta musamman kan harkokin siyasa

“Hannatu Musa Musawa mai ba da shawara ta musamman kan tattalin arziki da al’adu

Sai Sanata Abdullahi Abubakar Gumel, matsayin mai ba da shawara kan sha’anin majalisar dokokin Nijeriya (Dattijai)

“Hon. (Barr) Olarewaju Kunle Ibrahim, matsayin babban mataimaki na musamman a majalisar wakilai ta Kasa (Majalisar Wakilai)

A karshe shugaban kasar ya amince da nadin Adeniyi Bashir Adewale a matsayin mai rikon mukamin Kwanturola Janar na Kwastam.

Sai dai shugabannin hukumar da aka nada da sufeto-janar na ‘yan sanda da kuma babban kwanturolan hukumar kwastam za su yi aiki a kan mukamansu, har sai an tabbatar da su kamar yadda kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya ya tanada.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Tinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Johann Rupert Ya Doke Dangote A Matsayin Mutumin Da Ya Fi Kowa Kudi A Afirka

Next Post

Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Related

Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

10 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

16 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

17 hours ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

19 hours ago
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa
Manyan Labarai

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

19 hours ago
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

1 day ago
Next Post
Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.