• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Gudanar Da Bikin Ranar Yaki Da Sha Da Fataucin Miyagun Kwayoyi Na Duniya A Kebbi

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
NDLEA Ta Gudanar Da Bikin Ranar Yaki Da Sha Da Fataucin Miyagun Kwayoyi Na Duniya A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Hana Sha da Fataucin miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), reshen Jihar Kebbi, ta bi sahun sauran jihohi da masu ruwa da tsaki wajen gudanar da bikin ranar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta duniya a jihar.

Bayan kudurin Majalisar Dinkin Duniya (MDD) a shekarar 1987, ranar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi na duniya da nufin karfafa aiki da hadin gwiwa don cimma burin al’ummar duniya da ba ta su ga muggan kwayoyi.

  • Mutane 3 Sun Mutu A Hatsarin Mota, Biyu Sun Jikkata A Kogi
  • G7 Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Taimakon Ukraine A Yakinta Da Rasha

Bikin na 2022 mai taken cewa” Magance kalubalen shan kwayoyi a cikin Lafiya da Rikicin Jin kai yana da matukar dacewa dangane da cutar ta Korona da karuwar kalubalen tsaro a Nijeriya”.

 

A shekarar 2021, NDLEA ta kama sama da tan bakwai na haramtattun kwayoyi da kudinsu ya haura Naira Biliyan 130 tare da gurfanar da mutane sama da 900 da ake zargi.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

A nasa jawabin, Kwamandan NDLEA na shiyyar Sokoto, Kebbi da Zamfara, Muhammad Misbahu Idris, ya yabawa kokarin mai girma Sanata Abubakar Atiku Bagudu, da uwar gidansa Dakta Zainab Shinkafi Bagudu,  bisa gagarumin goyon baya da gudunmawar da suke bayarwa a Jihar Kebbi wajen ganin an magance matsalar na shan miyagun kwayoyi a fadin Jihar.

Haka kuma ya ce” yawaitar shaye-shayen miyagun kwayoyi a Nijeriya ya yi yawa, kafin yawan shan muggan kwayoyi a duniya ya kai kashi 15 cikin 100 amma a Nijeriya a yau ya kai kashi 15.

Haka zalika, ya yi kira ga iyaye da masu ruwa da tsaki da su zage damtse wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu wajen kula da ‘ya’yansu da kyau don kaucewa ga fadawa cikin shan miyagun kwayoyi ko kuma abokantaka da Matasa masu shaye shaye.

Bugu da kari, ya yi kira ga jami’an hukumarsa da su kara kaimi wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na kamawa da gurfanar da masu aikata laifin shan miyagun kwayoyi.

Tun da farko, kwamishinan ma’aikatar kiwon lafiya na jihar, Jafar Muhammad, wanda ya wakilci gwamnan jihar Kebbi, ya yi alkawarin ci gaba da bayar da goyon bayan gwamnatin jihar domin dakile ta’ammali da miyagun kwayoyi a jihar.

A wani bangare na bikin rana, an gudanar da atisayen tafiya da kafa da rera wakoki daga ofishin jiha zuwa fadar Sarkin Gwandu, daga nan sai suka zarce zuwa masaukin fadar shugaban kasa, inda aka gudanar da lakcoci kan shaye-shayen miyagun kwayoyi da laifuka, da kuma haramcin shan miyagun kwayoyi a cikin al’umma.

Mahalarta taron, sun hada da sakatare na dindindin na Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kebbi, Wakilan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, Hukumar Kula da Lafiyar Jama’a ta Tarayya, Jami’an Hukumar Kare Hadura ta Kasa, Jami’an Tsaro da Tsaron Farar Hula, Kungiyoyin Sa-kai da Kungiyoyin Jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukumar LafiyaKebbiKwamandaNDLEAShan Miyagun KwayoyiSokotoZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kafa Cibiyar Raya Al’Adu Da Tattalin Arzikin Sin Da Afrika A Fuzhou

Next Post

Dole Ne A Ci Gaba Da Binciken Alkalin Alkalai Mai Murabus, Tanko Muhammad — Majalisa

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

1 hour ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

2 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

2 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

3 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

6 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

6 hours ago
Next Post
Dole Ne A Ci Gaba Da Binciken Alkalin Alkalai Mai Murabus, Tanko Muhammad — Majalisa

Dole Ne A Ci Gaba Da Binciken Alkalin Alkalai Mai Murabus, Tanko Muhammad — Majalisa

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.