• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Amurka Ta Sake Komawa UNESCO Bayan Da Ta Sha Ficewa Daga Hukumar?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Amurka Ta Sake Komawa UNESCO Bayan Da Ta Sha Ficewa Daga Hukumar?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Amurka za ta sake komawa hukumar kula da ilmi da kimiyya da al’adu ta MDD, wato UNESCO a takaice. 

A ranar 30 ga watan Yuni, an zartas da wani daftarin kuduri yayin taron musamman na babban taron UNESCO, inda aka amince da maido da kujerar kasar Amurka a hukumar tun daga watan Yulin da ake ciki daga dukkanin fannoni. Hakan nan ya zama karo na uku da Amurka za ta kasance mamban hukumar, wato bayan da ta fice daga hukumar a shekarar 1984 da ta 2018.

  • Sin: Ya Dace Amurka Ta Ingiza Hada Kan UNESCO Bayan Dawowarta Hukumar

Amma me ya sa Amurka ta sake komawa hukumar? Me ya sa kuma ta sha komawa bayan ficewa?

Wata kila muna iya gano amsar tambayar daga jawabin da mataimakin sakataren harkokin wajen kasar John Bass ya yi, a gun taron manema labarai da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta gudanar a watan Maris da ya gabata, inda ya ce, a ganin gwamnatin kasar Amurka, komawa hukumar UNESCO zai taimakawa Amurka wajen takarar da take yi da kasar Sin a duniya.

A hakika, a cikin ’yan shekarun baya, Amurka ta sha ficewa da kuma komawa hukumomi, da yarjejeniyoyi na kasa da kasa. Idan ba a manta ba, baya ga UNESCO, Amurka ta kuma fice daga yarjejeniyar Paris, da yarjejeniyar bakin haure ta duniya, da yarjejeniyar nukiliya ta Iran, da majalisar hakkin dan Adam ta MDD, da hukumar lafiya ta duniya da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

In dai mun yi nazari a kan dalilin ficewarta da komarta kuma, za mu gano cewa, kullum tana neman kujera a kungiyoyin duniya ne don biyan bukatunta, amma idan ba ta cimma buri ba sa ta fice. Lallai, don cimma moriyarta, da ma kiyaye babakeren da ta kafa ne take shiga kungiyoyin duniya.

Sai dai kuma neman wakilci a kungiyoyin duniya ba wasa ba ne, kuma bai kamata a mai da shi a matsayin dabarar yin takara da wasu don cimma burin siyasa ba.

Idan dai da sahihiyar zuci ne Amurka ke son komawa a wannan karo, to, ya kamata ta sauke nauyin da ke wuyanta, ta biya kudin karo-karo na hukumar yadda ya kamata, sa’an nan ta kiyaye cudanyar da ke tsakanin bangarori daban daban, da ma ikon mulki, da tsarinsu na mabanbantan kasashe, ta yi kokarin inganta fahimtar juna, da hadin gwiwa da tsakanin kasashe kambobin hukumar, don tinkarar kalubale na bai daya da duniyarmu ke fuskanta. (Mai Zane: Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gwiwa Da Sin Na Ingiza Ci Gaban Kasashen Afirka, In Ji Wani Kwararre

Next Post

Gidan Yari Da Amurka Ta Kafa A Ketare Ya Keta Hakkin Bil Adama

Related

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

4 hours ago
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 
Daga Birnin Sin

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

5 hours ago
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

6 hours ago
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

7 hours ago
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

8 hours ago
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

9 hours ago
Next Post
Gidan Yari Da Amurka Ta Kafa A Ketare Ya Keta Hakkin Bil Adama

Gidan Yari Da Amurka Ta Kafa A Ketare Ya Keta Hakkin Bil Adama

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.