• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Yafe Wa Kowa, Ina Rokon Yafiyar Kowa —Sheikh Dahiru Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Na Yafe Wa Kowa, Ina Rokon Yafiyar Kowa —Sheikh Dahiru Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fitaccen malamin Darika a Afrika, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya ce, dukkanin wani mutumin da ya taba masa wani laifi to ya sha kuruminsa domin kuwa ya yafe wa kowa. 

A daidai lokacin da yake yafe wa mutane, shi ma ya roki dukkanin wani da ya masa wani laifi da ya taimaka ya yafe masa domin a cewarsa ya riga ya gama samun biyan bukatu na abubuwan da yake burin samu a wajen Allah illa guda daya.

  • NCAA Ta Dakatar Da Max Air Daga Jigilar Fasinjoji A Nijeriya
  • Yau Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Emefiele Ya Shigar

Kodayake ga sauran dayan ma, Sheikh Dahiru Bauchi ya yi fata da rokon Allah cika masa. Ya ce, babban abun alfahari a gareshi yadda ya kyankyashe zakakuran mahahaddata Alkur’ani mai girma da babu adadi.

Daya daga cikin ‘ya’yan malamin, Sayyid Ali Sheikh Dahiru Bauchi shi ne ya shelanta wa duniya wannan yafiyar na mahaifinsa a lokacin da ke jawabi a wajen wani taron karrama daliban da suka kammala karatun Alkur’ani na makarantar Sayyid Ali da suka koyi Kira’a a ranar Alhamis.

 

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Ya ce, “Ina mana albishir na cewa Maulana Sheikh ya ji irin karatun da almajiransa suke yi, ya saurara yana bibiya, ya ji suna karatu da kira’o’i da dama da yawa, ya ce wannan abun ya masa dadi, masa dadi saboda ya san kur’ani kenan na nan. Ya ce amma da yana fargaba.

“To amma da ya ga haka abun ya faranta masa rai duk damuwowinsa da suke damunsa sun fita daga zuciyarsa. Saboda haka ya ce a dalilin wannan jin dadin yake cewa ya karrama wadannan bayanin Allah da suka tsaya tsayin daka wajen koyar da wadannan da sauransu.”

“Ya ce tun da aka masa abun da aka masa a Kaduna bai samu nutsuwa mai dadi ba sai da ya ji karatun yara suna kira’o’u daban-daban da takbili ya ji abun ya masa dadi sosai, saboda dalilin haka, albishir din da ya mana, ya ce, ya yafe wa kowa; duk dan Nijeriya da ma na duniya gaba daya, ya yafe masa in akwai wani abu a tsakaninsu.

“Shi kuma yana rokon in akwai wani da ya masa wani abu yana rokon don Allah a yafe masa. Abun da yake neman ke nan, saboda shi ya ce dukkanin burinsa ya gama cika. Duk abun da yake nema a wajen Allah, Allah ya masa saura guda daya.”

“Don haka ya ce ya riga ya yafe wa duk wani da yake da wani abu a tsakaninsu shi ma na neman hakan saboda yana son ya gamu da Allah lafiya.”

Sayyid Ali ya ya gode wa mahaifinsu bisa hidimar da ya ke yi wa addini. Ya kuma yaba ma wadanda suka rike amana wajen tafiyar da dukkanin amanar da Shehi ya ba su musamman na koyarwa.

Sai ya taya wadanda suka samu karatun murna da cewa za a karramasu da kyautuka daban-daban masu daraja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DarikaMalamiSheikh Dahiru Bauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

NCAA Ta Dakatar Da Max Air Daga Jigilar Fasinjoji A Nijeriya

Next Post

Yanzu-yanzu: Everton Ta Dauki Ashley Young Daga Aston Villa

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

5 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

5 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

6 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

7 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

9 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

10 hours ago
Next Post
Yanzu-yanzu: Everton Ta Dauki Ashley Young Daga Aston Villa

Yanzu-yanzu: Everton Ta Dauki Ashley Young Daga Aston Villa

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.