ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

by Sadiq
1 year ago
Dantata

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana rasuwar attajiri kuma mai taimakon al’umma, Alhaji Aminu Dantata, a matsayin babban rashi ba kawai ga Jihar Kano ba, har ma ga Nijeriya da Nahiyar Afirka baki ɗaya. 

Ya yaba da irin gudummawar da Dantata ya bayar wajen bunƙasa tattalin arziƙi da samar da ayyukan yi.

  • Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi
  • Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

A cikin wata sanarwa daga ofishin yaɗa labaransa, Atiku ya ce ya ji matuƙar baƙin ciki da rasuwar wannan gogaggen ɗan kasuwa wanda ya shahara sosai a Nijeriya da Afirka.

ADVERTISEMENT

“Aminu Dantata ya kasance sanannen ɗan kasuwa na tsawon shekaru da dama. Ya zaburar da matasa da dama su shiga harkar kasuwanci,” in ji Atiku.

“Ba za a iya tattauna harkokin kasuwanci a Nijeriya ba tare da an ambaci sunan dangin Dantata ba.”

LABARAI MASU NASABA

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

Atiku, wanda ya tsaya takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP a 2023, ya bayyana Dantata a matsayin jarumin da ke ɗaukar kasada a harkokin kasuwanci, wanda ya ce wata muhimmiyar ɗabi’a ce ta manyan masu saka hannun jari.

Ya yaba da yadda Dantata ya sauya kasuwancin danginsu daga saye da sayarwa ta hanyar gargajiya zuwa aikin gine-gine da injiniyanci na zamani, wanda hakan ya samar da dubban ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya.

Atiku ya kuma nuna girmamawa ga Dantata bisa irin taimakon da yake yi wa jama’a cikin sirri ba tare da neman ɗaukaka ko yabo ba.

“Ya kasance mai dukiya sosai amma bai taɓa nuna girman kai ba, wannan ɗabi’a ce da ba kowa ke da ita ba,” in ji Atiku.

“Ya kasance abin koyi kuma tushen ƙarfafawa ga mutane da dama.”

Ya ƙara da cewa Dantata mutum ne mai son zaman lafiya wanda ya guji maganganun da ke kawo rabuwar kau, kuma ya jajirce wajen ƙarfafa zaman lafiya a tsakanin ‘yan Nijeriya.

Atiku ya shawarci Gwamnatin Tarayya da ta girmama Dantata ta hanyar sanya sunansa a wani muhimmin gini ko cibiyar gwamnati, domin tunawa da gudunmawarsa ga ci gaban al’umma da tattalin arziƙin ƙasa.

MASU ALAKA

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule
Manyan Labarai

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026
Next Post
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026
Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

July 21, 2026
Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.