ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Yafe Wa Kowa, Ina Rokon Yafiyar Kowa —Sheikh Dahiru Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Fitaccen malamin Darika a Afrika, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya ce, dukkanin wani mutumin da ya taba masa wani laifi to ya sha kuruminsa domin kuwa ya yafe wa kowa. 

A daidai lokacin da yake yafe wa mutane, shi ma ya roki dukkanin wani da ya masa wani laifi da ya taimaka ya yafe masa domin a cewarsa ya riga ya gama samun biyan bukatu na abubuwan da yake burin samu a wajen Allah illa guda daya.

  • NCAA Ta Dakatar Da Max Air Daga Jigilar Fasinjoji A Nijeriya
  • Yau Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Emefiele Ya Shigar

Kodayake ga sauran dayan ma, Sheikh Dahiru Bauchi ya yi fata da rokon Allah cika masa. Ya ce, babban abun alfahari a gareshi yadda ya kyankyashe zakakuran mahahaddata Alkur’ani mai girma da babu adadi.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin ‘ya’yan malamin, Sayyid Ali Sheikh Dahiru Bauchi shi ne ya shelanta wa duniya wannan yafiyar na mahaifinsa a lokacin da ke jawabi a wajen wani taron karrama daliban da suka kammala karatun Alkur’ani na makarantar Sayyid Ali da suka koyi Kira’a a ranar Alhamis.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Ya ce, “Ina mana albishir na cewa Maulana Sheikh ya ji irin karatun da almajiransa suke yi, ya saurara yana bibiya, ya ji suna karatu da kira’o’i da dama da yawa, ya ce wannan abun ya masa dadi, masa dadi saboda ya san kur’ani kenan na nan. Ya ce amma da yana fargaba.

“To amma da ya ga haka abun ya faranta masa rai duk damuwowinsa da suke damunsa sun fita daga zuciyarsa. Saboda haka ya ce a dalilin wannan jin dadin yake cewa ya karrama wadannan bayanin Allah da suka tsaya tsayin daka wajen koyar da wadannan da sauransu.”

“Ya ce tun da aka masa abun da aka masa a Kaduna bai samu nutsuwa mai dadi ba sai da ya ji karatun yara suna kira’o’u daban-daban da takbili ya ji abun ya masa dadi sosai, saboda dalilin haka, albishir din da ya mana, ya ce, ya yafe wa kowa; duk dan Nijeriya da ma na duniya gaba daya, ya yafe masa in akwai wani abu a tsakaninsu.

“Shi kuma yana rokon in akwai wani da ya masa wani abu yana rokon don Allah a yafe masa. Abun da yake neman ke nan, saboda shi ya ce dukkanin burinsa ya gama cika. Duk abun da yake nema a wajen Allah, Allah ya masa saura guda daya.”

“Don haka ya ce ya riga ya yafe wa duk wani da yake da wani abu a tsakaninsu shi ma na neman hakan saboda yana son ya gamu da Allah lafiya.”

Sayyid Ali ya ya gode wa mahaifinsu bisa hidimar da ya ke yi wa addini. Ya kuma yaba ma wadanda suka rike amana wajen tafiyar da dukkanin amanar da Shehi ya ba su musamman na koyarwa.

Sai ya taya wadanda suka samu karatun murna da cewa za a karramasu da kyautuka daban-daban masu daraja.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Yanzu-yanzu: Everton Ta Dauki Ashley Young Daga Aston Villa

Yanzu-yanzu: Everton Ta Dauki Ashley Young Daga Aston Villa

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.