ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Yafe Wa Kowa, Ina Rokon Yafiyar Kowa —Sheikh Dahiru Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Fitaccen malamin Darika a Afrika, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya ce, dukkanin wani mutumin da ya taba masa wani laifi to ya sha kuruminsa domin kuwa ya yafe wa kowa. 

A daidai lokacin da yake yafe wa mutane, shi ma ya roki dukkanin wani da ya masa wani laifi da ya taimaka ya yafe masa domin a cewarsa ya riga ya gama samun biyan bukatu na abubuwan da yake burin samu a wajen Allah illa guda daya.

  • NCAA Ta Dakatar Da Max Air Daga Jigilar Fasinjoji A Nijeriya
  • Yau Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Emefiele Ya Shigar

Kodayake ga sauran dayan ma, Sheikh Dahiru Bauchi ya yi fata da rokon Allah cika masa. Ya ce, babban abun alfahari a gareshi yadda ya kyankyashe zakakuran mahahaddata Alkur’ani mai girma da babu adadi.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin ‘ya’yan malamin, Sayyid Ali Sheikh Dahiru Bauchi shi ne ya shelanta wa duniya wannan yafiyar na mahaifinsa a lokacin da ke jawabi a wajen wani taron karrama daliban da suka kammala karatun Alkur’ani na makarantar Sayyid Ali da suka koyi Kira’a a ranar Alhamis.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

Ya ce, “Ina mana albishir na cewa Maulana Sheikh ya ji irin karatun da almajiransa suke yi, ya saurara yana bibiya, ya ji suna karatu da kira’o’i da dama da yawa, ya ce wannan abun ya masa dadi, masa dadi saboda ya san kur’ani kenan na nan. Ya ce amma da yana fargaba.

“To amma da ya ga haka abun ya faranta masa rai duk damuwowinsa da suke damunsa sun fita daga zuciyarsa. Saboda haka ya ce a dalilin wannan jin dadin yake cewa ya karrama wadannan bayanin Allah da suka tsaya tsayin daka wajen koyar da wadannan da sauransu.”

“Ya ce tun da aka masa abun da aka masa a Kaduna bai samu nutsuwa mai dadi ba sai da ya ji karatun yara suna kira’o’u daban-daban da takbili ya ji abun ya masa dadi sosai, saboda dalilin haka, albishir din da ya mana, ya ce, ya yafe wa kowa; duk dan Nijeriya da ma na duniya gaba daya, ya yafe masa in akwai wani abu a tsakaninsu.

“Shi kuma yana rokon in akwai wani da ya masa wani abu yana rokon don Allah a yafe masa. Abun da yake neman ke nan, saboda shi ya ce dukkanin burinsa ya gama cika. Duk abun da yake nema a wajen Allah, Allah ya masa saura guda daya.”

“Don haka ya ce ya riga ya yafe wa duk wani da yake da wani abu a tsakaninsu shi ma na neman hakan saboda yana son ya gamu da Allah lafiya.”

Sayyid Ali ya ya gode wa mahaifinsu bisa hidimar da ya ke yi wa addini. Ya kuma yaba ma wadanda suka rike amana wajen tafiyar da dukkanin amanar da Shehi ya ba su musamman na koyarwa.

Sai ya taya wadanda suka samu karatun murna da cewa za a karramasu da kyautuka daban-daban masu daraja.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Next Post
Yanzu-yanzu: Everton Ta Dauki Ashley Young Daga Aston Villa

Yanzu-yanzu: Everton Ta Dauki Ashley Young Daga Aston Villa

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.