• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Yafe Wa Kowa, Ina Rokon Yafiyar Kowa —Sheikh Dahiru Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Na Yafe Wa Kowa, Ina Rokon Yafiyar Kowa —Sheikh Dahiru Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fitaccen malamin Darika a Afrika, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya ce, dukkanin wani mutumin da ya taba masa wani laifi to ya sha kuruminsa domin kuwa ya yafe wa kowa. 

A daidai lokacin da yake yafe wa mutane, shi ma ya roki dukkanin wani da ya masa wani laifi da ya taimaka ya yafe masa domin a cewarsa ya riga ya gama samun biyan bukatu na abubuwan da yake burin samu a wajen Allah illa guda daya.

  • NCAA Ta Dakatar Da Max Air Daga Jigilar Fasinjoji A Nijeriya
  • Yau Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Emefiele Ya Shigar

Kodayake ga sauran dayan ma, Sheikh Dahiru Bauchi ya yi fata da rokon Allah cika masa. Ya ce, babban abun alfahari a gareshi yadda ya kyankyashe zakakuran mahahaddata Alkur’ani mai girma da babu adadi.

Daya daga cikin ‘ya’yan malamin, Sayyid Ali Sheikh Dahiru Bauchi shi ne ya shelanta wa duniya wannan yafiyar na mahaifinsa a lokacin da ke jawabi a wajen wani taron karrama daliban da suka kammala karatun Alkur’ani na makarantar Sayyid Ali da suka koyi Kira’a a ranar Alhamis.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Ya ce, “Ina mana albishir na cewa Maulana Sheikh ya ji irin karatun da almajiransa suke yi, ya saurara yana bibiya, ya ji suna karatu da kira’o’i da dama da yawa, ya ce wannan abun ya masa dadi, masa dadi saboda ya san kur’ani kenan na nan. Ya ce amma da yana fargaba.

“To amma da ya ga haka abun ya faranta masa rai duk damuwowinsa da suke damunsa sun fita daga zuciyarsa. Saboda haka ya ce a dalilin wannan jin dadin yake cewa ya karrama wadannan bayanin Allah da suka tsaya tsayin daka wajen koyar da wadannan da sauransu.”

“Ya ce tun da aka masa abun da aka masa a Kaduna bai samu nutsuwa mai dadi ba sai da ya ji karatun yara suna kira’o’u daban-daban da takbili ya ji abun ya masa dadi sosai, saboda dalilin haka, albishir din da ya mana, ya ce, ya yafe wa kowa; duk dan Nijeriya da ma na duniya gaba daya, ya yafe masa in akwai wani abu a tsakaninsu.

“Shi kuma yana rokon in akwai wani da ya masa wani abu yana rokon don Allah a yafe masa. Abun da yake neman ke nan, saboda shi ya ce dukkanin burinsa ya gama cika. Duk abun da yake nema a wajen Allah, Allah ya masa saura guda daya.”

“Don haka ya ce ya riga ya yafe wa duk wani da yake da wani abu a tsakaninsu shi ma na neman hakan saboda yana son ya gamu da Allah lafiya.”

Sayyid Ali ya ya gode wa mahaifinsu bisa hidimar da ya ke yi wa addini. Ya kuma yaba ma wadanda suka rike amana wajen tafiyar da dukkanin amanar da Shehi ya ba su musamman na koyarwa.

Sai ya taya wadanda suka samu karatun murna da cewa za a karramasu da kyautuka daban-daban masu daraja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DarikaMalamiSheikh Dahiru Bauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

NCAA Ta Dakatar Da Max Air Daga Jigilar Fasinjoji A Nijeriya

Next Post

Yanzu-yanzu: Everton Ta Dauki Ashley Young Daga Aston Villa

Related

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

9 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

11 hours ago
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
Labarai

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

12 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

13 hours ago
Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

14 hours ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

17 hours ago
Next Post
Yanzu-yanzu: Everton Ta Dauki Ashley Young Daga Aston Villa

Yanzu-yanzu: Everton Ta Dauki Ashley Young Daga Aston Villa

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.