• English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       

by CMG Hausa
2 years ago
wang yi

Babban jami’in diflomasiyyar kasar Sin Wang Yi, ya bayyana cewa, kamata ya yi Amurka ta dauki kwararan matakai don dawo da dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka kan hanyar da ta dace.

Wang, daraktan ofishin hukumar kula da harkokin wajen na kwamitin kolin JKS ya bayyana hakan ne jiya Alhamis, yayin ganawarsa da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a gefen taron ministocin harkokin wajen kungiyar ASEAN. Yana mai cewa, bangarorin biyu sun cimma matsaya ta hanyar zurfafa tattaunawa ta gaskiya, yayin ziyarar da Blinken ya kawo kasar Sin a watan da ya gabata.

  • Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Ya kara da cewa, muhimmiyar yarjejeniya ita ce komawa kan ajandar da shugabannin kasashen biyu suka cimma a tsibirin Bali na kasar Indonesiya, da daukar muhimmin mataki na tsara tsarin da ya dace wajen inganta alakar manyan kasashen biyu

Wang ya yi karin haske kan matsayar kasar Sin game da batun yankin Taiwan, inda ya bukaci Amurka da ta guji tsoma baki a harkokin cikin gidan kasar Sin ba gaira ba dalili, ko kuma yin zagon kasa ga ikon mulkinta da ma cikakkun yankunanta, da dakatar da dakile ci gabanta ta fuskar tattalin arziki, da cinikayya, da harkokin kimiyya da fasaha, da mayar da kasar Sin saniyar ware, kana ta cire dukkan takunkumai na babu gaira babu dalili da ta kakkaba mata.

Game da wannan ganawa, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin ya bayyana a yau cewa, Wang Yi ya bayyana matsayin Sin kan tsaron yanar gizo da yaki da miyagun kwayoyi a yayin ganawar.

LABARAI MASU NASABA

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Wang Wenbin ya kara da cewa, kasar Sin tana tinkarar hare-hare ta yanar gizo da ake kai wa hukumominta a kowace rana, kuma yawancinsu daga Amurka. Ya ce Sin kasa ce da ta fi fama da hare-hare ta yanar gizo, don haka, bai kamata Amurka ta zarge ta kan wannan batu ba.

Ban da wannan kuma, Wang ya ce, Sin da Amurka sun yi tattaunawa kan batun maganin Fentanyl a yayin ganawar, inda Sin ta bayyana matsayinta da damuwarta. Wang Yi ya yi nuni da cewa, Sin ta fi tsayawa tsayin daka kan manufar yaki da miyagun kwayoyi a duniya, amma Amurka ba ta amince da kokarin Sin a wannan fanni ba, tana zargin Sin da amfani da irin maganin, da kuma kama mutanen Sin ba bisa doka ba. Ya ce ya kamata Amurka ta daidaita batun bisa yanayin na adalci da girmamawa da hadin gwiwa, da soke takunkumin da ta sakawa hukumomin Sin masu kula da ayyukan yaki da miyagun kwayoyi cikin hanzari, don kawar da cikas ga shawarwari da hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu. (Ibrahim Yaya, Zainab)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 
Daga Birnin Sin

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Next Post
Shin Amurka Na Son Maimaita Laifukan Da Ta Aikata A Kan Al’ummar Laos A Rikicin Ukraine?

Shin Amurka Na Son Maimaita Laifukan Da Ta Aikata A Kan Al'ummar Laos A Rikicin Ukraine?

LABARAI MASU NASABA

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

November 10, 2025
FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.