• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
in Wasanni
0
Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Pierre Emeric Aubameyang ya kammala komawa kungiyar kwallon kafa ta Olympique Marseille da ke kasar Faransa.

Dan wasan Gabon, mai shekaru 34, ya ci kwallaye uku kacal a wasanni 22 da ya buga wa Chelsea, bayan da ya koma daga Barcelona kan kudi fam miliyan 10.3 a watan Satumban da ta gabata.

  • Rusau: Kotu Ta Ci Tarar Gwamnatin Kano Naira Miliyan 2
  • Hajjin 2023: NAHCON Za Ta Kammala Dawo Da Alhazan Nijeriya A Watan Agusta

Babu wata shaida da ta bayyana ko Marseille ta biya kudin dan wasan wanda haifaffen Faransa ne.

Aubameyang ya fice daga gasar Firimiyar Ingila a karo na biyu cikin watanni 18, bayan ya shafe shekaru hudu a Arsenal daga 2018 kafin ya koma Barcelona a watan Janairun 2022.

Ya zura kwallaye 13 a wasanni 23 a cikin watanni shida da ya yi a Barcelona, amma ya kasa tabuka abin azo a gani a Stamford Bridge.

Labarai Masu Nasaba

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Gwarzon dan kwallon Afrika na 2015, ya buga wasa daya kacal a karkashin Thomas Tuchel, tsohon kocinsa a Borussia Dortmund, kafin a kore shi tare da maye gurbinsa da Graham Potter.

Kwallaye uku a wasanni uku da ya buga a watan Oktoba ya nuna yiwuwar dawowa fagen daga, amma Aubameyang ya kasa sake zura kwallo a raga.

An cire shi daga cikin ‘yan wasan da za su buga gasar zakarun Turai a gasar cin kofin zakarun Turai bayan da aka sayo sabbin ‘yan wasa a watan Janairu, ciki har da ‘yan wasan gaba Mykhailo Mudryk da Noni Madueke.

Aubameyang ya koma gasar Ligue 1 ta kasar Faransa bayan barinta shekaru 10 da suka gabata, inda ya lashe Coupe de la Ligue a 2013 a Monaco.

Aubameyang shi ne dan wasan Chelsea na bakwai da ya bar kungiyar a bana.

Dan wasan tsakiya na Croatia Mateo Kovacic ya koma Manchester City, Kai Havertz ya koma Arsenal sannan Mason Mount ya koma Manchester United, yayin da mai tsaron gida Edouard Mendy da mai tsaron baya Kalidou Koulibaly suka koma kungiyar Al-Ahli ta Saudiyya.

N’Golo Kante ya koma Saudiyya, inda ya koma Al-Ittihad, yayin da ‘yan wasan tsakiya Ruben Loftus-Cheek da Christian Pulisic suka koma AC Milan, shi kuma kyaftin din Cesar Azpilicueta ya koma Atletico Madrid.

Blues ta sayi dan wasan gaba na Brazil Angelo Gabriel, mai shekara 18 daga Santos, dan wasan Faransa Christopher Nkunku, mai shekara 25, daga RB Leipzig, da dan wasan Senegal Nicolas Jackson mai shekara 22 daga Villarreal.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AubameyangChelseaFaransaKwallon Kafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rusau: Kotu Ta Ci Tarar Gwamnatin Kano Naira Miliyan 2

Next Post

Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

Related

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
Wasanni

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

7 hours ago
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan
Wasanni

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

9 hours ago
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal
Wasanni

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

10 hours ago
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

2 days ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

4 days ago
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

6 days ago
Next Post
Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Aubameyang

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.