• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kai Hari Wani Coci A Osun

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kai Hari Wani Coci A Osun
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talatar da ta gabata ne aka gurfanar da wasu mutum uku a shalkwatar ‘yan sandan Jihar Osun da ake zargi a harin da aka kai a wata Cocin Celestial da ke kauyen Odu kusa da Osogbo.

An cafke wadanda ake zargin sun kai hari cocin ne a lokacin da suke sintiri da sanyin safiyar Talata.

  • Rikicin Nijar: Tinubu Ya Aika Janar Abdulsalami, Sultan Na Sokoto Zuwa Yamai
  • Me Ya Haifar Da Koma Bayan Ababen More Rayuwa A Kasar Amurka?

A yayin harin, wadanda suka kai harin sun yi awon gaba da mabiya cocin 12, amma wadanda abin ya shafa sun gudu daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su a lokacin da suka ci karo da wasu mafarauta da kuma wasu masu aikin sa kai na yankin da aka kira su suka zo cikin gaggawa.

A yayin faruwar lamarin, an ruwaito cewa wadanda suka aikata laifin sun yi wa wata ‘yar cocin fyade wacca ba a bayyana sunan ta ba.

Da take ba da labarin abin da ya faru, wata mawakiyar coci, wanda Fasto mai kula da cocin ya gayyace ta mai suna Esther Ayodeji, yayin wata tattaunawa da jaridar PUNCH Metro ta ce, “Na isa cocin ‘yan mintuna kadan bayan karfe 10 na dare a ranar Litinin don wasu ayyukan da suka shafi coci. Mun fara sintiri ne da tsakar dare. Bayan kammala dukkan hidima tare da masu ganguna sauran wasu mutane na cikin cocin, amma saina fita.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

“Bayan ‘yan mintoci kadan, daga inda na tsaya tare da limamin cocin, muka fara jin harbe-harbe a ciki, mun shiga wani yanayi mai cike da rudani, don haka, duk sai muka gudu cikin daji. Cikin wadanda muka gudu sai muka hadu a daji mu bakwai, shida mata da namiji daya. Muna cikin yawo a cikin daji, sai ga wasu mutane biyu dauke da makamai suka bayyana a gabanmu, duk muka tarwatse da gudu wurare daban-daban”.

Wani mamba a cocin da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce an kai wacce aka yi wa fyaden  asibiti, inda ya kara da cewa a wannan lokacin dai lamarin na su basu samu nasara ba nasara ba saboda saurin daukin mutanen kauyen da mafarauta da jami’an ‘yan sanda suka kawo.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Yemisi Opalola, wanda ya shawarci kungiyoyin addini da su guji yin shirye-shirye da yamma ko kuma safiya, musamman a cibiyoyi da ke a kebabbun wurare, ya ce ana ci gaba da yi wa mutane uku da aka kama a kusa da wurin tambayoyi.

Da yake gabatar da sauran wadanda ake zargi da suka hada da wadanda aka kama da laifin zama mambobin kungiyoyi haratattu da suka hada da fashi da makami, Opalola ya ce Adebayo Adedayo da Adeyemi Sodik sun kai wa wani dan kasuwa hari a Iragbiji inda suka sace kudi da kayayyaki da aka kiyasta sun kai kimanin Naira 877,000.

Ta kara da cewa Yusuf Baoku da Ajayi Ismail, wadanda aka kama da laifin yunkurin kisan kai da kuma zama mambobin haramtacciyar kungiya, za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

Next Post

Nigeria Air Zai Fara Aiki A Watan Oktoba —Ethiopian Airlines

Related

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

2 weeks ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

2 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

3 weeks ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

4 months ago
Next Post
Nigeria Air Zai Fara Aiki A Watan Oktoba —Ethiopian Airlines

Nigeria Air Zai Fara Aiki A Watan Oktoba —Ethiopian Airlines

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.