ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kai Hari Wani Coci A Osun

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Osun

A ranar Talatar da ta gabata ne aka gurfanar da wasu mutum uku a shalkwatar ‘yan sandan Jihar Osun da ake zargi a harin da aka kai a wata Cocin Celestial da ke kauyen Odu kusa da Osogbo.

An cafke wadanda ake zargin sun kai hari cocin ne a lokacin da suke sintiri da sanyin safiyar Talata.

  • Rikicin Nijar: Tinubu Ya Aika Janar Abdulsalami, Sultan Na Sokoto Zuwa Yamai
  • Me Ya Haifar Da Koma Bayan Ababen More Rayuwa A Kasar Amurka?

A yayin harin, wadanda suka kai harin sun yi awon gaba da mabiya cocin 12, amma wadanda abin ya shafa sun gudu daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su a lokacin da suka ci karo da wasu mafarauta da kuma wasu masu aikin sa kai na yankin da aka kira su suka zo cikin gaggawa.

ADVERTISEMENT

A yayin faruwar lamarin, an ruwaito cewa wadanda suka aikata laifin sun yi wa wata ‘yar cocin fyade wacca ba a bayyana sunan ta ba.

Da take ba da labarin abin da ya faru, wata mawakiyar coci, wanda Fasto mai kula da cocin ya gayyace ta mai suna Esther Ayodeji, yayin wata tattaunawa da jaridar PUNCH Metro ta ce, “Na isa cocin ‘yan mintuna kadan bayan karfe 10 na dare a ranar Litinin don wasu ayyukan da suka shafi coci. Mun fara sintiri ne da tsakar dare. Bayan kammala dukkan hidima tare da masu ganguna sauran wasu mutane na cikin cocin, amma saina fita.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

“Bayan ‘yan mintoci kadan, daga inda na tsaya tare da limamin cocin, muka fara jin harbe-harbe a ciki, mun shiga wani yanayi mai cike da rudani, don haka, duk sai muka gudu cikin daji. Cikin wadanda muka gudu sai muka hadu a daji mu bakwai, shida mata da namiji daya. Muna cikin yawo a cikin daji, sai ga wasu mutane biyu dauke da makamai suka bayyana a gabanmu, duk muka tarwatse da gudu wurare daban-daban”.

Wani mamba a cocin da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce an kai wacce aka yi wa fyaden  asibiti, inda ya kara da cewa a wannan lokacin dai lamarin na su basu samu nasara ba nasara ba saboda saurin daukin mutanen kauyen da mafarauta da jami’an ‘yan sanda suka kawo.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Yemisi Opalola, wanda ya shawarci kungiyoyin addini da su guji yin shirye-shirye da yamma ko kuma safiya, musamman a cibiyoyi da ke a kebabbun wurare, ya ce ana ci gaba da yi wa mutane uku da aka kama a kusa da wurin tambayoyi.

Da yake gabatar da sauran wadanda ake zargi da suka hada da wadanda aka kama da laifin zama mambobin kungiyoyi haratattu da suka hada da fashi da makami, Opalola ya ce Adebayo Adedayo da Adeyemi Sodik sun kai wa wani dan kasuwa hari a Iragbiji inda suka sace kudi da kayayyaki da aka kiyasta sun kai kimanin Naira 877,000.

Ta kara da cewa Yusuf Baoku da Ajayi Ismail, wadanda aka kama da laifin yunkurin kisan kai da kuma zama mambobin haramtacciyar kungiya, za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike.

Osun
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Nigeria Air Zai Fara Aiki A Watan Oktoba —Ethiopian Airlines

Nigeria Air Zai Fara Aiki A Watan Oktoba —Ethiopian Airlines

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.