ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kai Hari Wani Coci A Osun

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Osun

A ranar Talatar da ta gabata ne aka gurfanar da wasu mutum uku a shalkwatar ‘yan sandan Jihar Osun da ake zargi a harin da aka kai a wata Cocin Celestial da ke kauyen Odu kusa da Osogbo.

An cafke wadanda ake zargin sun kai hari cocin ne a lokacin da suke sintiri da sanyin safiyar Talata.

  • Rikicin Nijar: Tinubu Ya Aika Janar Abdulsalami, Sultan Na Sokoto Zuwa Yamai
  • Me Ya Haifar Da Koma Bayan Ababen More Rayuwa A Kasar Amurka?

A yayin harin, wadanda suka kai harin sun yi awon gaba da mabiya cocin 12, amma wadanda abin ya shafa sun gudu daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su a lokacin da suka ci karo da wasu mafarauta da kuma wasu masu aikin sa kai na yankin da aka kira su suka zo cikin gaggawa.

ADVERTISEMENT

A yayin faruwar lamarin, an ruwaito cewa wadanda suka aikata laifin sun yi wa wata ‘yar cocin fyade wacca ba a bayyana sunan ta ba.

Da take ba da labarin abin da ya faru, wata mawakiyar coci, wanda Fasto mai kula da cocin ya gayyace ta mai suna Esther Ayodeji, yayin wata tattaunawa da jaridar PUNCH Metro ta ce, “Na isa cocin ‘yan mintuna kadan bayan karfe 10 na dare a ranar Litinin don wasu ayyukan da suka shafi coci. Mun fara sintiri ne da tsakar dare. Bayan kammala dukkan hidima tare da masu ganguna sauran wasu mutane na cikin cocin, amma saina fita.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

“Bayan ‘yan mintoci kadan, daga inda na tsaya tare da limamin cocin, muka fara jin harbe-harbe a ciki, mun shiga wani yanayi mai cike da rudani, don haka, duk sai muka gudu cikin daji. Cikin wadanda muka gudu sai muka hadu a daji mu bakwai, shida mata da namiji daya. Muna cikin yawo a cikin daji, sai ga wasu mutane biyu dauke da makamai suka bayyana a gabanmu, duk muka tarwatse da gudu wurare daban-daban”.

Wani mamba a cocin da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce an kai wacce aka yi wa fyaden  asibiti, inda ya kara da cewa a wannan lokacin dai lamarin na su basu samu nasara ba nasara ba saboda saurin daukin mutanen kauyen da mafarauta da jami’an ‘yan sanda suka kawo.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Yemisi Opalola, wanda ya shawarci kungiyoyin addini da su guji yin shirye-shirye da yamma ko kuma safiya, musamman a cibiyoyi da ke a kebabbun wurare, ya ce ana ci gaba da yi wa mutane uku da aka kama a kusa da wurin tambayoyi.

Da yake gabatar da sauran wadanda ake zargi da suka hada da wadanda aka kama da laifin zama mambobin kungiyoyi haratattu da suka hada da fashi da makami, Opalola ya ce Adebayo Adedayo da Adeyemi Sodik sun kai wa wani dan kasuwa hari a Iragbiji inda suka sace kudi da kayayyaki da aka kiyasta sun kai kimanin Naira 877,000.

Ta kara da cewa Yusuf Baoku da Ajayi Ismail, wadanda aka kama da laifin yunkurin kisan kai da kuma zama mambobin haramtacciyar kungiya, za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike.

Osun
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Nigeria Air Zai Fara Aiki A Watan Oktoba —Ethiopian Airlines

Nigeria Air Zai Fara Aiki A Watan Oktoba —Ethiopian Airlines

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.