ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kai Hari Wani Coci A Osun

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Osun

A ranar Talatar da ta gabata ne aka gurfanar da wasu mutum uku a shalkwatar ‘yan sandan Jihar Osun da ake zargi a harin da aka kai a wata Cocin Celestial da ke kauyen Odu kusa da Osogbo.

An cafke wadanda ake zargin sun kai hari cocin ne a lokacin da suke sintiri da sanyin safiyar Talata.

  • Rikicin Nijar: Tinubu Ya Aika Janar Abdulsalami, Sultan Na Sokoto Zuwa Yamai
  • Me Ya Haifar Da Koma Bayan Ababen More Rayuwa A Kasar Amurka?

A yayin harin, wadanda suka kai harin sun yi awon gaba da mabiya cocin 12, amma wadanda abin ya shafa sun gudu daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su a lokacin da suka ci karo da wasu mafarauta da kuma wasu masu aikin sa kai na yankin da aka kira su suka zo cikin gaggawa.

ADVERTISEMENT

A yayin faruwar lamarin, an ruwaito cewa wadanda suka aikata laifin sun yi wa wata ‘yar cocin fyade wacca ba a bayyana sunan ta ba.

Da take ba da labarin abin da ya faru, wata mawakiyar coci, wanda Fasto mai kula da cocin ya gayyace ta mai suna Esther Ayodeji, yayin wata tattaunawa da jaridar PUNCH Metro ta ce, “Na isa cocin ‘yan mintuna kadan bayan karfe 10 na dare a ranar Litinin don wasu ayyukan da suka shafi coci. Mun fara sintiri ne da tsakar dare. Bayan kammala dukkan hidima tare da masu ganguna sauran wasu mutane na cikin cocin, amma saina fita.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

“Bayan ‘yan mintoci kadan, daga inda na tsaya tare da limamin cocin, muka fara jin harbe-harbe a ciki, mun shiga wani yanayi mai cike da rudani, don haka, duk sai muka gudu cikin daji. Cikin wadanda muka gudu sai muka hadu a daji mu bakwai, shida mata da namiji daya. Muna cikin yawo a cikin daji, sai ga wasu mutane biyu dauke da makamai suka bayyana a gabanmu, duk muka tarwatse da gudu wurare daban-daban”.

Wani mamba a cocin da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce an kai wacce aka yi wa fyaden  asibiti, inda ya kara da cewa a wannan lokacin dai lamarin na su basu samu nasara ba nasara ba saboda saurin daukin mutanen kauyen da mafarauta da jami’an ‘yan sanda suka kawo.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Yemisi Opalola, wanda ya shawarci kungiyoyin addini da su guji yin shirye-shirye da yamma ko kuma safiya, musamman a cibiyoyi da ke a kebabbun wurare, ya ce ana ci gaba da yi wa mutane uku da aka kama a kusa da wurin tambayoyi.

Da yake gabatar da sauran wadanda ake zargi da suka hada da wadanda aka kama da laifin zama mambobin kungiyoyi haratattu da suka hada da fashi da makami, Opalola ya ce Adebayo Adedayo da Adeyemi Sodik sun kai wa wani dan kasuwa hari a Iragbiji inda suka sace kudi da kayayyaki da aka kiyasta sun kai kimanin Naira 877,000.

Ta kara da cewa Yusuf Baoku da Ajayi Ismail, wadanda aka kama da laifin yunkurin kisan kai da kuma zama mambobin haramtacciyar kungiya, za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike.

Osun
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Nigeria Air Zai Fara Aiki A Watan Oktoba —Ethiopian Airlines

Nigeria Air Zai Fara Aiki A Watan Oktoba —Ethiopian Airlines

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.