• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar Da Na Ba Tinubu Kan Tsadar Rayuwa A Nijeriya – Shugabar WTO

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Darakta Janar na hukumar kasuwanci ta duniya (WTO), Dakta Ngozi Okonlo-Iweala ta ce Nijeriya na bukatar bullo da shirye-shiryen da za su taimaka wa al’umma wajen samar da ayyukan yi ga matasa da mata.

Okonlo-Iweala ta bayyana hakan ne da take yi wa manema labarai jawabi a fadar shugaban kasa bayan ganawarta da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a ranar Talata, ta ce bullo da shirye-shirye na al’ummar kasa zai magance wasu matsalolin da ke addabar ‘yan Nijeriya a halin yanzu.

  • Gwamnatin Gombe Za Ta Dauki Sababbin Ma’aikatan Lafiya 200
  • Fasahar Zane-zane Na Iya Bunƙasa Samar Da Kuɗaɗen Waje Ga Nijeriya – CIS James 

“Mun ga shugaban kasa, kuma mun tattauna kan yadda za mu tallafa wa ‘yan Najeriya a wannan lokaci na bukata. Duk mun san cewa ‘yan Nijeriya na cikin matsanancin halin, kowa yana kokawa. Hakan ne ma ya sa na kawo wannan ziyara da kaina. Wannan ba aikin WTO ba ne a hukumance, amma mun sami damar tattaunawa da shugaban kasa kan irin shirye-shiryen da za a iya yi don tabbatar da cewa ana rage radadin da’yan Nijeriya ke sha.

“Mun gudanar da tattaunawa mai matukar muhimmanci kan kokarin bullo da tsare-tsare da za su taimaka wa al’umma wajen samar da ayyukan yi ga matasa, kuma tallafa wa mata da kananan yara, wadanda za su rage wasu wahalhalun da ake fama da su a cikin kasa.

“Mun yi magana na tsawon lokaci, muna bukatar samun damar saka hannun jari da Nijeriya za ta iya dogaro da kanta, ciki har da habaka masana’antar sarrafa magunguna. Mun kuma yi magana kan irin tallafin da hukumar kasuwanci ta duniya za ta iya kawowa.

“Mun yi aiki a Nijeriya tare da mata, musamman wadanda suka mallaki kanana da matsakaitan masana’antu don kokarin taimaka musu wajen inganta kayayyakinsu ta fannin noma, masaku da sauran fannoni domin su samu damar sayar da su da daraja a kasashen duniya.

“Muna kokarin taimaka musu ta fannin fasahar zamani, domin mu horar da matan Nijeriya da masu kananan sana’o’i da matsakaitan masana’antu wajen kara habaka kasuwancinsu da samar da ayyukan yi.

“Abin da muka tattauna da mai girma shugaban kasa kenan a matsayina ta darakta janar ta kungiyar kasuwanci ta duniya, za mu yi kokarin iya bakin  kokarinmu don tallafa wa ‘yan Nijeriya a wannan lokaci,” in ji ta.

An Cafke Masu Safarar Kwaya 214 Cikin Wata Bakwai A Gombe

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa reshen Jihar Gombe, ta ce ta kama mutum akalla 214 da take zargi da laifin safarar miyagun kwayoyi a jihar tsakanin watan Janairu zuwa Yuli.

Haka nan, an kama ‘Cannabis Satiba’ mai nauyin kilo giram 93.95, da kuma Kilo giram 257.5 na abubuwan da suka shafi ‘Psychotropic’ da Methamphetamine daga hannun wadanda ake zargin a wannan lokaci.

Kamfanin Dillancin Labarun Nijeriya ya ruwaito cewa Mataimakin Kwamandan Hukumar na Jihar, Bello Mumini ne ya bayyana hakan a wani taro da kungiyar kwararrun masu ba da shawara a Nijeriya ta shirya.

Da yake gabatar da kasidarsa mai taken “Halin da ake fama da shi game da ta’ammali da muggan kwayoyi a Jihar Gombe,” Mumini ya ce wadanda ake zargin 214 sun hada da maza 200 da mata 14.

Ya ce daga cikin mutum 214 da aka kama, 137 daga cikinsu an gurfanar da su a gaban kotu.

Jami’in Hukumar na NDLEA, ya yi tir da yadda ake fama da matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi a jihar, inda ya kara da cewa hakan yana tasir a tsakanin jinsi, cikin shekaru da kuma yin illa a zamantakewar al’umma.

Ya ce abin takaici ne yadda ake samun mata da dama suna shiga harkar shan miyagun kwayoyi a jihar.

 Ya kuma ce abin takaici ne da ya zamto ba a yin amfani da cibiyar gyaran hali ta NDLEA a jihar yadda ya kamata duk da yawaitar shan miyagun kwayoyi a jihar.

Ya ce, “Cibiyar gyaran hali ta NDLEA tana aiki amma ba a amfani da ita kamar yadda ya kamata.

“Muna da daki mai gadaje 24 amma mafi girman abin da muke samu shi ne mutum bakwai da ake tsarewa domin kula da gyaran hallaya da dabi’unsu.

“Wannan shi ne dalilin da ya sa nake kira ga gwamnatin jihar da gwamnatin tarayya da su tallafa wa cibiyar tare da tallafa wa ake kai wa wurin don inganta rayuwarsu.”

Mumini ta yaba wa kungiyar ta APROCON bisa gudanar da gangamin yaki da hana shaye-shayen miyagun kwayoyi a yayin da take yi wa matasa nasiha akan illar shan muggan kwayoyi da sauran abubuwan sa maye.

A nata bangaren, Shugabar Kungiyar ta APROCON, Dakta Habiba Isah, ta ce shaye-shayen miyagun kwayoyi ya zama wata barazana da ya kamata ta da mu da duk masu ruwa da tsaki mu shigo ciki domin ganin an magance irin illar da ke tattare da ita da kuma rayuwar matasa.

Ta ce kungiyarta ta kaddamar da yaki da wannan barna kuma za ta je wasu manyan makarantun jihar domin jawo hankalin matasa da kuma hana su shan miyagun kwayoyi ta hanyar nusar da su hanyoyin illar abin.

Isah, wacce kuma ita ce Shugabar Sashen, Gidauniyar Ilimi ta Tsangayar Ilimi ta Jami’ar Jihar Gombe, ta bukaci iyaye da su yi taka-tsan-tsan tare da kare ‘ya’yansu daga shan ta’ammali da miyagun kwayoyi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Gaggauta Gyara Kura-Kurai Da Bin Ka’idojin WTO

Next Post

’Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

Related

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

10 minutes ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

1 hour ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

6 hours ago
Tinubu
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

6 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

7 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Tinubu

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.