ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar Da Na Ba Tinubu Kan Tsadar Rayuwa A Nijeriya – Shugabar WTO

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Darakta Janar na hukumar kasuwanci ta duniya (WTO), Dakta Ngozi Okonlo-Iweala ta ce Nijeriya na bukatar bullo da shirye-shiryen da za su taimaka wa al’umma wajen samar da ayyukan yi ga matasa da mata.

Okonlo-Iweala ta bayyana hakan ne da take yi wa manema labarai jawabi a fadar shugaban kasa bayan ganawarta da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a ranar Talata, ta ce bullo da shirye-shirye na al’ummar kasa zai magance wasu matsalolin da ke addabar ‘yan Nijeriya a halin yanzu.

  • Gwamnatin Gombe Za Ta Dauki Sababbin Ma’aikatan Lafiya 200
  • Fasahar Zane-zane Na Iya Bunƙasa Samar Da Kuɗaɗen Waje Ga Nijeriya – CIS James 

“Mun ga shugaban kasa, kuma mun tattauna kan yadda za mu tallafa wa ‘yan Najeriya a wannan lokaci na bukata. Duk mun san cewa ‘yan Nijeriya na cikin matsanancin halin, kowa yana kokawa. Hakan ne ma ya sa na kawo wannan ziyara da kaina. Wannan ba aikin WTO ba ne a hukumance, amma mun sami damar tattaunawa da shugaban kasa kan irin shirye-shiryen da za a iya yi don tabbatar da cewa ana rage radadin da’yan Nijeriya ke sha.

“Mun gudanar da tattaunawa mai matukar muhimmanci kan kokarin bullo da tsare-tsare da za su taimaka wa al’umma wajen samar da ayyukan yi ga matasa, kuma tallafa wa mata da kananan yara, wadanda za su rage wasu wahalhalun da ake fama da su a cikin kasa.

“Mun yi magana na tsawon lokaci, muna bukatar samun damar saka hannun jari da Nijeriya za ta iya dogaro da kanta, ciki har da habaka masana’antar sarrafa magunguna. Mun kuma yi magana kan irin tallafin da hukumar kasuwanci ta duniya za ta iya kawowa.

“Mun yi aiki a Nijeriya tare da mata, musamman wadanda suka mallaki kanana da matsakaitan masana’antu don kokarin taimaka musu wajen inganta kayayyakinsu ta fannin noma, masaku da sauran fannoni domin su samu damar sayar da su da daraja a kasashen duniya.

“Muna kokarin taimaka musu ta fannin fasahar zamani, domin mu horar da matan Nijeriya da masu kananan sana’o’i da matsakaitan masana’antu wajen kara habaka kasuwancinsu da samar da ayyukan yi.

“Abin da muka tattauna da mai girma shugaban kasa kenan a matsayina ta darakta janar ta kungiyar kasuwanci ta duniya, za mu yi kokarin iya bakin  kokarinmu don tallafa wa ‘yan Nijeriya a wannan lokaci,” in ji ta.

An Cafke Masu Safarar Kwaya 214 Cikin Wata Bakwai A Gombe

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa reshen Jihar Gombe, ta ce ta kama mutum akalla 214 da take zargi da laifin safarar miyagun kwayoyi a jihar tsakanin watan Janairu zuwa Yuli.

Haka nan, an kama ‘Cannabis Satiba’ mai nauyin kilo giram 93.95, da kuma Kilo giram 257.5 na abubuwan da suka shafi ‘Psychotropic’ da Methamphetamine daga hannun wadanda ake zargin a wannan lokaci.

Kamfanin Dillancin Labarun Nijeriya ya ruwaito cewa Mataimakin Kwamandan Hukumar na Jihar, Bello Mumini ne ya bayyana hakan a wani taro da kungiyar kwararrun masu ba da shawara a Nijeriya ta shirya.

Da yake gabatar da kasidarsa mai taken “Halin da ake fama da shi game da ta’ammali da muggan kwayoyi a Jihar Gombe,” Mumini ya ce wadanda ake zargin 214 sun hada da maza 200 da mata 14.

Ya ce daga cikin mutum 214 da aka kama, 137 daga cikinsu an gurfanar da su a gaban kotu.

Jami’in Hukumar na NDLEA, ya yi tir da yadda ake fama da matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi a jihar, inda ya kara da cewa hakan yana tasir a tsakanin jinsi, cikin shekaru da kuma yin illa a zamantakewar al’umma.

Ya ce abin takaici ne yadda ake samun mata da dama suna shiga harkar shan miyagun kwayoyi a jihar.

 Ya kuma ce abin takaici ne da ya zamto ba a yin amfani da cibiyar gyaran hali ta NDLEA a jihar yadda ya kamata duk da yawaitar shan miyagun kwayoyi a jihar.

Ya ce, “Cibiyar gyaran hali ta NDLEA tana aiki amma ba a amfani da ita kamar yadda ya kamata.

“Muna da daki mai gadaje 24 amma mafi girman abin da muke samu shi ne mutum bakwai da ake tsarewa domin kula da gyaran hallaya da dabi’unsu.

“Wannan shi ne dalilin da ya sa nake kira ga gwamnatin jihar da gwamnatin tarayya da su tallafa wa cibiyar tare da tallafa wa ake kai wa wurin don inganta rayuwarsu.”

Mumini ta yaba wa kungiyar ta APROCON bisa gudanar da gangamin yaki da hana shaye-shayen miyagun kwayoyi a yayin da take yi wa matasa nasiha akan illar shan muggan kwayoyi da sauran abubuwan sa maye.

A nata bangaren, Shugabar Kungiyar ta APROCON, Dakta Habiba Isah, ta ce shaye-shayen miyagun kwayoyi ya zama wata barazana da ya kamata ta da mu da duk masu ruwa da tsaki mu shigo ciki domin ganin an magance irin illar da ke tattare da ita da kuma rayuwar matasa.

Ta ce kungiyarta ta kaddamar da yaki da wannan barna kuma za ta je wasu manyan makarantun jihar domin jawo hankalin matasa da kuma hana su shan miyagun kwayoyi ta hanyar nusar da su hanyoyin illar abin.

Isah, wacce kuma ita ce Shugabar Sashen, Gidauniyar Ilimi ta Tsangayar Ilimi ta Jami’ar Jihar Gombe, ta bukaci iyaye da su yi taka-tsan-tsan tare da kare ‘ya’yansu daga shan ta’ammali da miyagun kwayoyi.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.