• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Sa Barayi Suka Kashe Sheikh Albani Kuri

by Yunusa Isa
2 years ago
Albani

Wasu barayi hudu sun kutsa gidan fitaccen malamin addinin Musuluncin nan Sheikh Ibrahim Halliru Musa da aka fi sani da Albani Kuri cikin daren ranar Laraba inda suka yi masa kisan gilla.

Barayin sun kutsa gidan malamin ne dake Bobona a Anguwar Tabra ta Karamar Hukumar Akko rufe da fuskokinsu, inda suka bukaci ya basu kudi.

  • An Gudanr Da Taron Dadadden Kwamitin Kula Da Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afrika Ta Kudu
  • Birnin Jinhua Na Kara Kyautata Alaka Da Kasashen Afirka

Kakakin rundunar ‘yansanda a Jihar ASP Mahid Muazu Abubakar, ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin, yana mai cewa kawo lokacin hada wannan rahoto ba su kama kowa ba kan lamarin, amma bincike na ci gaba da gudana kamar yadda kwamishinan ‘yansandan jihar CP Okua Etim ya ba da umarni.

Mahid Mu’azu ya ce marigayin ya yi kokarin gane daya daga cikin barayin ne ta hanyar yaye fuskarsa dake rufe, lamarin da ya sa suka sassare shi da adda a wuya da kai da kuma baya, har ma da caccaka masa wuka a kirji.

Ficewarsu ke da wuya aka dauke shi zuwa asibiti, amma saboda munanan raunukan da suka yi masa ba a jima da isa asibitin ba ya rasu.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Shugaban kungiyar Izala a jihar Sheikh Salisu Muhammad Gombe ya yi Allah wadai tare da bayyana takaici kan kisan, yana mai bayyana rashin Sheikh Albani Kuri a matsayin babban rashi ga al’ummar Musulmi baki daya.

Yace suna fatan binciken da jami’an tsaro ke yi zai haifar da da mai ido ta hanyar kamowa da hukunta wadanda suka aikata wannan danyen aika-aika.

Marigayi malamin addinin Musuluncin ya rasu yana da shekaru 46, ya bar mata biyu da ‘ya’ya hudu da mahaifiyarsa da kuma ‘yan uwa da dama.

Tuni dai aka yi jana’izar Marigayi Sheikh Albani Kuri a masallacin Izala da ke Bolari, wadda ya samu halartar dubban jama’a daga nesa da kusa ciki har da gwamnan jihar Muhammadu Inuwa Yahaya.

A baya bayan nan dai ana samun karuwar shiga gidaje da kwacen waya da sauran miyagun laifuka a jihar, lamarin da masharhanta ke danganta shi da rashin ayyukan yi da zaman banza tsakanin matasa.

Suna ganin kara tsaurara tsaro da samarwa matasa abun yi ka iya taimakawa matuka wajen rage matsalar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

LABARAI MASU NASABA

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.