ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Sa Barayi Suka Kashe Sheikh Albani Kuri

by Yunusa Isa
3 years ago
Albani

Wasu barayi hudu sun kutsa gidan fitaccen malamin addinin Musuluncin nan Sheikh Ibrahim Halliru Musa da aka fi sani da Albani Kuri cikin daren ranar Laraba inda suka yi masa kisan gilla.

Barayin sun kutsa gidan malamin ne dake Bobona a Anguwar Tabra ta Karamar Hukumar Akko rufe da fuskokinsu, inda suka bukaci ya basu kudi.

  • An Gudanr Da Taron Dadadden Kwamitin Kula Da Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afrika Ta Kudu
  • Birnin Jinhua Na Kara Kyautata Alaka Da Kasashen Afirka

Kakakin rundunar ‘yansanda a Jihar ASP Mahid Muazu Abubakar, ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin, yana mai cewa kawo lokacin hada wannan rahoto ba su kama kowa ba kan lamarin, amma bincike na ci gaba da gudana kamar yadda kwamishinan ‘yansandan jihar CP Okua Etim ya ba da umarni.

ADVERTISEMENT

Mahid Mu’azu ya ce marigayin ya yi kokarin gane daya daga cikin barayin ne ta hanyar yaye fuskarsa dake rufe, lamarin da ya sa suka sassare shi da adda a wuya da kai da kuma baya, har ma da caccaka masa wuka a kirji.

Ficewarsu ke da wuya aka dauke shi zuwa asibiti, amma saboda munanan raunukan da suka yi masa ba a jima da isa asibitin ba ya rasu.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Shugaban kungiyar Izala a jihar Sheikh Salisu Muhammad Gombe ya yi Allah wadai tare da bayyana takaici kan kisan, yana mai bayyana rashin Sheikh Albani Kuri a matsayin babban rashi ga al’ummar Musulmi baki daya.

Yace suna fatan binciken da jami’an tsaro ke yi zai haifar da da mai ido ta hanyar kamowa da hukunta wadanda suka aikata wannan danyen aika-aika.

Marigayi malamin addinin Musuluncin ya rasu yana da shekaru 46, ya bar mata biyu da ‘ya’ya hudu da mahaifiyarsa da kuma ‘yan uwa da dama.

Tuni dai aka yi jana’izar Marigayi Sheikh Albani Kuri a masallacin Izala da ke Bolari, wadda ya samu halartar dubban jama’a daga nesa da kusa ciki har da gwamnan jihar Muhammadu Inuwa Yahaya.

A baya bayan nan dai ana samun karuwar shiga gidaje da kwacen waya da sauran miyagun laifuka a jihar, lamarin da masharhanta ke danganta shi da rashin ayyukan yi da zaman banza tsakanin matasa.

Suna ganin kara tsaurara tsaro da samarwa matasa abun yi ka iya taimakawa matuka wajen rage matsalar.

Albani
Yunusa Isa
+ postsBio
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Gwamnatin Gombe Za Ta Dauki Sababbin Ma’aikatan Lafiya 200
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Gwamnatin Gombe Ta Sha Alwashin Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Gwamnatin Gombe Ta Bukaci Jami’an Lafiya Da Su Kara Kwazo Wajen Yaki Da Cutar Sida
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    FRSC Ta Buɗe Sabin Rassa A Ɓilliri Da Dukku A Jihar Gombe

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.