ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Sa Barayi Suka Kashe Sheikh Albani Kuri

by Yunusa Isa
3 years ago
Albani

Wasu barayi hudu sun kutsa gidan fitaccen malamin addinin Musuluncin nan Sheikh Ibrahim Halliru Musa da aka fi sani da Albani Kuri cikin daren ranar Laraba inda suka yi masa kisan gilla.

Barayin sun kutsa gidan malamin ne dake Bobona a Anguwar Tabra ta Karamar Hukumar Akko rufe da fuskokinsu, inda suka bukaci ya basu kudi.

  • An Gudanr Da Taron Dadadden Kwamitin Kula Da Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afrika Ta Kudu
  • Birnin Jinhua Na Kara Kyautata Alaka Da Kasashen Afirka

Kakakin rundunar ‘yansanda a Jihar ASP Mahid Muazu Abubakar, ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin, yana mai cewa kawo lokacin hada wannan rahoto ba su kama kowa ba kan lamarin, amma bincike na ci gaba da gudana kamar yadda kwamishinan ‘yansandan jihar CP Okua Etim ya ba da umarni.

ADVERTISEMENT

Mahid Mu’azu ya ce marigayin ya yi kokarin gane daya daga cikin barayin ne ta hanyar yaye fuskarsa dake rufe, lamarin da ya sa suka sassare shi da adda a wuya da kai da kuma baya, har ma da caccaka masa wuka a kirji.

Ficewarsu ke da wuya aka dauke shi zuwa asibiti, amma saboda munanan raunukan da suka yi masa ba a jima da isa asibitin ba ya rasu.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Shugaban kungiyar Izala a jihar Sheikh Salisu Muhammad Gombe ya yi Allah wadai tare da bayyana takaici kan kisan, yana mai bayyana rashin Sheikh Albani Kuri a matsayin babban rashi ga al’ummar Musulmi baki daya.

Yace suna fatan binciken da jami’an tsaro ke yi zai haifar da da mai ido ta hanyar kamowa da hukunta wadanda suka aikata wannan danyen aika-aika.

Marigayi malamin addinin Musuluncin ya rasu yana da shekaru 46, ya bar mata biyu da ‘ya’ya hudu da mahaifiyarsa da kuma ‘yan uwa da dama.

Tuni dai aka yi jana’izar Marigayi Sheikh Albani Kuri a masallacin Izala da ke Bolari, wadda ya samu halartar dubban jama’a daga nesa da kusa ciki har da gwamnan jihar Muhammadu Inuwa Yahaya.

A baya bayan nan dai ana samun karuwar shiga gidaje da kwacen waya da sauran miyagun laifuka a jihar, lamarin da masharhanta ke danganta shi da rashin ayyukan yi da zaman banza tsakanin matasa.

Suna ganin kara tsaurara tsaro da samarwa matasa abun yi ka iya taimakawa matuka wajen rage matsalar.

Albani
Yunusa Isa
+ postsBio
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Gwamnatin Gombe Za Ta Dauki Sababbin Ma’aikatan Lafiya 200
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Gwamnatin Gombe Ta Sha Alwashin Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Gwamnatin Gombe Ta Bukaci Jami’an Lafiya Da Su Kara Kwazo Wajen Yaki Da Cutar Sida
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    FRSC Ta Buɗe Sabin Rassa A Ɓilliri Da Dukku A Jihar Gombe

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.