ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bauchi Ta Kori Ma’aikata 2 Kan Amfani Da Takardun Bogi Don Cinye Kudin Mamaci

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Hukumar Kula Da Ma’aikata ta jihar Bauchi ta sake korar wasu ma’aikatan gwamnati biyu masu suna Nasiru Samaila da Anas Jibrin bisa samunsu da laifin amfani da takardun bogi domin cinye ma wani mamacin kudadensa. 

Ma’aikatan biyu, su na aiki ne a karkashin ma’aikatar kudi ta jihar an zargesu da karkatarwa da sama da fadi da naira N332, 000 mallakin wani tsohon ma’aikatacin ma’aikatar Jibrin Adamu Zalanga (wanda ya rasu ma a halin yanzu) wanda a cewar hukumar, wannan dabi’ar ta saba wa sashin dokokin aikin gwamnati sashi na 327.

  • Wakilin Jaridar Leadership Na Kano Ya Rasu
  • Kalubalen Hada Kan ‘Ya’yan Jam’iyyar APC Da Ke Gaban Ganduje 

Hukumar ta cimma wannan matsalar korar nasu ne a yayin zamanta karo na 18 da ya gudana a ranar 15 ga watan Agustan 2023.

ADVERTISEMENT

A sanarwar manema labarai da jami’in yada labarai na hukumar Saleh Umar ya fitar a ranar Juma’a ya ce, “A yayin zaman da hukumar ta yi kan kes din kwamitin kula da ladabtarwa, ma’aikata guda biyu wanda aka samu da laifin amfani da takardun jabu domin samun damar karkatar da kudi da yawansu ya kai N332,000 mallakin wani tsoho kuma marigayin ma’aikacin ma’aikatar kudi na jihar Bauchi (Jibrin Adamu Zalanga)”.

“Wannan matakin nasu ya saba wa sashi 327 na dokokin tsarin aikin gwamnati kuma jami’an biyu sun amsa laifukansu a yayin amsa tambayoyin da ma’aikatar ta musu,” Umar ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

Malam Saleh Umar ya yi kuma yi bayanin cewa tun da farko ‘yansanda sun kama ma’aikatan biyu tare da gurfanar da su a gaban babban kotun majistire domin samun hukunci daidai da laifukansu.

A cewarsa a yayin zaman hukumar ta kuma amince da karin girma ga wasu jami’ai 73 bisa kwazonsu da cancantarsu, kana an yi sauyi ga wasu mutum 11.

Shugaban hukumar, Alhaji Abubakar Usman Madakin Bunun Bauchi wanda ya jagoranci zaman, ya ce, kesa-kesan badakar kudade da suke samu na matukar damunsu.

Ya gargadi ma’aikata da suke jin tsoron Allah a dukkanin ayyukansu inda ya ce duk wanda ya kuma ki ji to ba zai ki gani ba.

A fadinsa za su kara sanya ido wajen dakile irin wannan mummunar dabi’ar.

Idan za ku tuna dai a kwanakin baya hukumar ta dakatar da izinin daukan aikin Ibrahim Garba wanda ma’aikaci ne a hukumar kula da fansho ta jihar bisa kamasa da laifin cinye kudin wani mamacin dan fansho.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
Labarai

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Next Post
Sin: Kasashen Sin Da Afirka Za Su Nuna Abin Misali Wajen Inganta Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Daukacin Bil-Adama

Sin: Kasashen Sin Da Afirka Za Su Nuna Abin Misali Wajen Inganta Gina Al'umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Daukacin Bil-Adama

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.