• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Musulmi Ga Malamai: Ku Rika Shawartar Masu Mulki Kan Shugabanci Nagari

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Sarkin Musulmi Ga Malamai: Ku Rika Shawartar Masu Mulki Kan Shugabanci Nagari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Abubakar ya bukaci malamai da su rika shawartar masu mulki kan shugabanci nagari.

Sarkin Musulmin ya yi wannan kiran ne a Abuja wajen taron bitar ga malaman addini kan harkokin kiwon lafiya a matakin farko.

  • Ranar Litinin Za A Kaddamar Da Jirgin Kasan Legas Da Zai Rika Jigilar Fasinja 175,000
  • NIS Ta Bude Ofishin Samar Da Ingantaccen Fasfo A Zariya

Kamfanin dillancin labara na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa ma’aikatar lafiya da jin dadin jama’a ta tarayya tare da hadin gwiwar hukumar kula da lafiya matakin farko ta kasa (NPHCDA) ne suka shirya taron.

Sarkin Musulmi ya ce yana da kyau malamai su kasance masu gaskiya da rikon amana a yayin da suke da kusanci da shugabannin siyasa.

“Shugabannin addini sukan rike mukamai masu gwabi kuma suna iya kawo sauyi ga rayuwar al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

“Ta hanyar ba da shawara ta gaskiya ne za a iya samun ingantacciyar shugabanci da zai ba da gudummawa ga rayuwar al’ummarsu gaba daya.

“Kyakkyawan sadarwa tsakanin malamai da shugabannin siyasa na iya haifar da fahimtar juna, hadin kai da kuma cimma manufofin da aka saka a gaba.

“A duk lokacin da malamai ke fada wa masu mulki gaskiya, zai taimaka wajen yanke hukunci da manufofi wadanda suka dogara a kan ingantattun bayanai da suka dace da dabi’u da ka’idodi,” in ji shi.

Shi ma shugaban kungiyar Kiristocin Nijeriya (CAN) Archbishop Daniel Okoh, ya bukaci karin hadin kai da hukumar kula da lafiya matakin farko ta kasa domin inganta harkokin kiwon lafiya musamman a yankunan karkara.

 Okoh, wanda ya bayyana muhimmiyar rawar da malaman addini suke takawa wajen bayar da shawarwari da wayar da kan jama’a, ya ce dole ne a hada kai da shugabannin siyasa domin inganta harkar kiwon lafiyar kasar nan.

Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Ali Pate, ya yaba wa gudunmawar da malamai ke bayarwa wajen samar da kiwon lafiya a kasar nan.

Ministan ya jaddada mahimmancin hadin gwiwa tsakanin gwamnati da malaman addini.

Pate ya ja hankali kan yadda fannin kiwon lafiya ke ci gaba da bunkasa, ya ce akwai bukatar yin hadin gwiwa a tsakanin ma’aikatan kiwon lafiya da malamai.

“Ta hanyar hadin kai ne za a samu damar ilimantar da juna da kuma sanar da jama’a game da abubuwan da ke faruwa, za mu tabbatar da cewa an samar da ayyuka masu inganci na kiwon lafiya ga ‘yan Nijeriya,” in ji shi.

Babban daraktan hukumar NPHCDA, Dakta Faisal Shuaib, ya yi kira ga malamai da su ba da himma gudunmuwa wajen inganta harkokin kiwon lafiya a matakin farko da kyautata jin dadin al’umma.

“Manufar wannan taro na musamman shi ne, rigakafin cutar kansa ta mahaifa ta hanyar allurer HPB,” in ji shi.

Ya bukaci shugabannin addini da su bayar da shawarwarin rigakafi a cibiyoyinsu.

Shugaban NPHCDA ya jaddada karfin hadin kai da aiki tare wajen inganta lafiya da walwalan al’umma.

Ya ce ta hanyar hada kai ne malamai da ma’aikatan kiwon lafiya za su bayar da gudummuwa ga harkokin lafiya da kuma ci gaban kasa.

NAN ta ruwaito cewa taron ya samu halartar malaman addini, ma’aikatan lafiya da masu ruwa da tsaki kan harkokin lafiya da manyan jami’an gudanarwa na ma’aikatar lafiya da NPHCDA.

Taron dai an yi shi ne domin kara inganta fahimtar malamai game da allurar rigakafi da sauran shirye-shiryen kiwon lafiya tare da wayar da kan al’umma kan amfanin rigakafin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Fara Shirin Aikewa Da Sinawa Zuwa Duniyar Wata Nan Zuwa 2030

Next Post

Amurka Tana Goyon Bayan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Yayin Da Ta Rage Shigo Da Kaya Daga Japan

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

8 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Sarkin Musulmi
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Japan

Amurka Tana Goyon Bayan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Yayin Da Ta Rage Shigo Da Kaya Daga Japan

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Sarkin Musulmi

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.