• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Tsawon Shekaru: Hada-Hadar Shanu Da Rakuma Ta Farfado A Jihar Yobe 

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Shanu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babu wani sauran sabon labari na kai hare-haren ‘yan kungiyar Boko Haram a gonakin manoma da dama a a Jihar Yobe, wanda sakamakon hare-haren ‘yan ta’addar a baya ya haifar da samun karancin abinci a jihohin da ke shiyyar Arewa Maso Gabashin wannan kasa.

Amma a ‘yan kwanakin baya, ayyukan kasuwancin dabbobi sun fara dawowa ka’in da na’in, inda ‘yan kasuwa daga sassa daban-daban na kasar nan ke zuwa Jihar Yobe domin sayen kayan abinci da kuma dabbobi.

  • Jami’an NSCDC Sun Cafke Matashin Da Ya Sace Babur Din Abokin Mahaifinsa
  • NNPP Na Zargin Kwankwaso Da Hannu Wajen Nasarar Gawuna Da Kwace Zaben Kano A Kotu

Wasu daga cikin ‘yan kasuwa a Kananan Hukumomin Potiskum, Geidam da kuma Damaturu a jihar sun tabbatar da cewa, duk da kalubalen rashin tsaro da jihar ta fuskanta a baya da kuma wasu sassan jihar, amma a yanzu kasauwancin dabbobin ta dawo.

Daya daga cikin ‘yan kasuwa kuma Sarkin Turakin Potiskum, Lamido Damina Yarima ya bayyana cewa, kafin hare-haren ‘yan Boko Haram, sama da motar tirela 50 a duk mako ke zuwa kasuwar shanu ta Potiskum, domin kwasar shanu zuwa wasu sassan Nijeriya, wanda a yanzu haka duk mako ake jigilar dabbobi a kasuwar kasa da guda 40. Ya ce, a yanzu ana zuwa kasuwar jihar ana sayen dabbobi da sauran kayan amfanin gona a duk mako.

Shi ma a nasa jawabin, Shugaban Kungiyar Mahauta na Potiskum Alhaji Ibrahim Yunusa Mali ya bayyana da cewa, a 2005 zuwa 2008, sama da Shanu 50 zuwa 80 mahauta suke yankawa a Potiskum, amma yanzu kasa da 20 kacal ake iya yankawa a kullum.

Labarai Masu Nasaba

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Ya ce, amma yanzu da ayyukan ‘yan kugiyar Boko Haram suka kawo karshe, hada-hadar kasuwanci ta dawo ganin cewa, jama’a na ci gaba da yin kasuwancinsu.

Kazalika, wani mai sayar da dabbobi a kasuwar Mallam Bana Aramma, ya sanar da cewa hada-hadar kasuwanci na kara ci gaba tare da habaka a kasuwar ganin yadda ayyukan ‘yan Boko Haram din suka zama tarihi.

Shi ma Saleh Damniya Gamdu, Maino da Jakana sun ce, sama da Tirala 50 na shanu ake jigilar daga kasuwar Kura-Reta da ke Jihar ta Yobe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Satar ShanuShanu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hasashe Yadda Wasan Manchester United Da Burnley Zai Kaya

Next Post

Zargin Daura Aure Da Mai Kanjamau: Yadda Aka Tube Hakimi A Katsina

Related

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

1 hour ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

7 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

1 week ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

1 week ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

1 week ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Next Post
Kanjamau

Zargin Daura Aure Da Mai Kanjamau: Yadda Aka Tube Hakimi A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.