• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Tsawon Shekaru: Hada-Hadar Shanu Da Rakuma Ta Farfado A Jihar Yobe 

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Shanu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babu wani sauran sabon labari na kai hare-haren ‘yan kungiyar Boko Haram a gonakin manoma da dama a a Jihar Yobe, wanda sakamakon hare-haren ‘yan ta’addar a baya ya haifar da samun karancin abinci a jihohin da ke shiyyar Arewa Maso Gabashin wannan kasa.

Amma a ‘yan kwanakin baya, ayyukan kasuwancin dabbobi sun fara dawowa ka’in da na’in, inda ‘yan kasuwa daga sassa daban-daban na kasar nan ke zuwa Jihar Yobe domin sayen kayan abinci da kuma dabbobi.

  • Jami’an NSCDC Sun Cafke Matashin Da Ya Sace Babur Din Abokin Mahaifinsa
  • NNPP Na Zargin Kwankwaso Da Hannu Wajen Nasarar Gawuna Da Kwace Zaben Kano A Kotu

Wasu daga cikin ‘yan kasuwa a Kananan Hukumomin Potiskum, Geidam da kuma Damaturu a jihar sun tabbatar da cewa, duk da kalubalen rashin tsaro da jihar ta fuskanta a baya da kuma wasu sassan jihar, amma a yanzu kasauwancin dabbobin ta dawo.

Daya daga cikin ‘yan kasuwa kuma Sarkin Turakin Potiskum, Lamido Damina Yarima ya bayyana cewa, kafin hare-haren ‘yan Boko Haram, sama da motar tirela 50 a duk mako ke zuwa kasuwar shanu ta Potiskum, domin kwasar shanu zuwa wasu sassan Nijeriya, wanda a yanzu haka duk mako ake jigilar dabbobi a kasuwar kasa da guda 40. Ya ce, a yanzu ana zuwa kasuwar jihar ana sayen dabbobi da sauran kayan amfanin gona a duk mako.

Shi ma a nasa jawabin, Shugaban Kungiyar Mahauta na Potiskum Alhaji Ibrahim Yunusa Mali ya bayyana da cewa, a 2005 zuwa 2008, sama da Shanu 50 zuwa 80 mahauta suke yankawa a Potiskum, amma yanzu kasa da 20 kacal ake iya yankawa a kullum.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

Ya ce, amma yanzu da ayyukan ‘yan kugiyar Boko Haram suka kawo karshe, hada-hadar kasuwanci ta dawo ganin cewa, jama’a na ci gaba da yin kasuwancinsu.

Kazalika, wani mai sayar da dabbobi a kasuwar Mallam Bana Aramma, ya sanar da cewa hada-hadar kasuwanci na kara ci gaba tare da habaka a kasuwar ganin yadda ayyukan ‘yan Boko Haram din suka zama tarihi.

Shi ma Saleh Damniya Gamdu, Maino da Jakana sun ce, sama da Tirala 50 na shanu ake jigilar daga kasuwar Kura-Reta da ke Jihar ta Yobe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Satar ShanuShanu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hasashe Yadda Wasan Manchester United Da Burnley Zai Kaya

Next Post

Zargin Daura Aure Da Mai Kanjamau: Yadda Aka Tube Hakimi A Katsina

Related

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

10 hours ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

11 hours ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

6 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

2 weeks ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

2 weeks ago
Next Post
Kanjamau

Zargin Daura Aure Da Mai Kanjamau: Yadda Aka Tube Hakimi A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.