• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halittar Mata Na Canzawa Bayan Aure

by Amina Usman
2 years ago
in Nazari
0
Halittar Mata Na Canzawa Bayan Aure
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda aka sani cewa kowace mace da irin kirar halittar da Ubangiji ya yi mata, amma tambayar a nan ita ce me ya sa mata ke murjewa su yi kiba bayan sun yi aure.

Wannan lamari ba bako ba ne ga dukkan al’ummar kasar Hausa. In muka duba za mu ga cewa da yawa daga cikin matan Nijeriya musammam yankin Arewa da zarar mace ta yi aure ba jimawa sai ka ga halittar jikinta ya fara sauyawa ta yi kiba ta murmure duk taya ni muni sun bace. A al’adance al’ummar kasar Hausa suna kallon wannan lamari a matsayin ci gaba ga mace saboda ana ganin cewar tana samun matukar kulawa a wurin mijinta.

  • Za Mu Tabbatar An Hukunta Masu Zaluntar Kananan Yara Da Mata – Kwamishina Rabi Salisu
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da ‘Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki

Amma sai dai abin tambaya a nan shi ne kulawar miji ita ce babbar magana da ke sa jikin mace ya canza ko kuwa akwai wasu abubuwa?

Tabbas kulawar miji na janyo sauyi ga halittar mace amma hakan bai isa dalili daya da za a ce shi ne ke janyo wannan sauyi ba.

Ga kadan daga cikin dalilan da ke sa mace samun sauyin halitta a gidan miji;

Labarai Masu Nasaba

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

Masana Sun Bayyana Yadda Yakin Neman Zaben 2027 Ke Barazana Ga Harkokin Tafiyar Da Gwamnati

Samin kwanciyar hankali

A lokacin da mace ta yi aure za a ga cewa akwai wata kwanciyar hankali na musamman da za ta fuskanta wanda duk inda ta je ba za ta same ta ba sai a gidan miji ire-iren wannan sauyi sun hada da amarci, soyayya, sannan kuma cima mai kyau, wadannan abubuwa suna da matukar tasiri a canjin halittar mace, cikin kankanin lokaci za a ga mace ta murmure ta murje.

Sabuwar Rayuwa da kuma samun ‘yancin kai

Bayan soyayya a aure akwai kuma wasu tarin nauyi da zai hau kan mace wanda hakan kansa ta fahimci cewar girma da kulawar wasu mutane ya hau kanta kamar su rainon ciki, haihuwa da kuma renon yaron da za ta haifa. Wannan sauyin da kwanciyar hankali suma suna kara taimaka wa mace wajen zama babbar mata. Sai a ga cikin kankanin lokaci mace ta murje ta yi jiki duk wasu jijiyoyi, kasusuwa, da kuma kwayar halittunta sun sami sauyi sun bude wanda hakan zai sa alamar kiba ta bayyana.

Rainon Ciki

Bayan hidimar aure akwai babbar hidima a gaban ma’aurata, wannan hidima ita ce daukar ciki. Haihuwa da aba ce mai matukar dadi da sa farin ciki kuma tana daga cikin abubuwa mafi sauki da ke kara wa mata budewar jiki ka ga sun yi kiba.

Daga lokacin da mace ta sami ciki to tabbas cin abincinta zai karu fiye da na da, za a ga idan a da tana cin karamin kwano to daga ta sami ciki sai ka ga abin ya canza, dole a nemo babban mazubi.

Mata yayin da suke da ciki suna matukar yin ciye-ciye sosai musamman abubuwa masu maiko wanda hakan ke sa jikin mace ya bude har ta yi jiki ta murmure.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2034: Nijeriya Na Goyon Bayan Saudiyya Ta Dauki Nauyin Kofin Duniya

Next Post

Sin Za Ta Fadada Girman Tashar Binciken Samaniyarta

Related

Mataimakin shugaban kasa
Nazari

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

16 hours ago
haraji
Nazari

Masana Sun Bayyana Yadda Yakin Neman Zaben 2027 Ke Barazana Ga Harkokin Tafiyar Da Gwamnati

1 month ago
Mata
Nazari

Shirin Fim Kan Cikar Nijeriya Shekaru 25 A Kan Turbar Dimokuradiyya: Tasiri Da Muhimmanci

2 months ago
Asalin Tushen Matsalolinmu A Nijeriya
Nazari

Asalin Tushen Matsalolinmu A Nijeriya

8 months ago
Sinadarin Ƙara Kuzari Lokacin Jima’i
Nazari

Sinadarin Ƙara Kuzari Lokacin Jima’i

12 months ago
Mata
Labarai

Farashin Shinkafa, Tumatir Da Gari Ya Qaru Da Kashi 141 Cikin Shekara Guda – NBS

12 months ago
Next Post
Sin

Sin Za Ta Fadada Girman Tashar Binciken Samaniyarta

LABARAI MASU NASABA

FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

June 3, 2025
FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

June 3, 2025
An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

AlÆ™alai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.