ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halittar Mata Na Canzawa Bayan Aure

by Amina Usman
3 years ago
Mata

Kamar yadda aka sani cewa kowace mace da irin kirar halittar da Ubangiji ya yi mata, amma tambayar a nan ita ce me ya sa mata ke murjewa su yi kiba bayan sun yi aure.

Wannan lamari ba bako ba ne ga dukkan al’ummar kasar Hausa. In muka duba za mu ga cewa da yawa daga cikin matan Nijeriya musammam yankin Arewa da zarar mace ta yi aure ba jimawa sai ka ga halittar jikinta ya fara sauyawa ta yi kiba ta murmure duk taya ni muni sun bace. A al’adance al’ummar kasar Hausa suna kallon wannan lamari a matsayin ci gaba ga mace saboda ana ganin cewar tana samun matukar kulawa a wurin mijinta.

  • Za Mu Tabbatar An Hukunta Masu Zaluntar Kananan Yara Da Mata – Kwamishina Rabi Salisu
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da ‘Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki

Amma sai dai abin tambaya a nan shi ne kulawar miji ita ce babbar magana da ke sa jikin mace ya canza ko kuwa akwai wasu abubuwa?

ADVERTISEMENT

Tabbas kulawar miji na janyo sauyi ga halittar mace amma hakan bai isa dalili daya da za a ce shi ne ke janyo wannan sauyi ba.

Ga kadan daga cikin dalilan da ke sa mace samun sauyin halitta a gidan miji;

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Siyasar 2027: Yadda Ƴan Adawa Ke Ƙara Shiga Tsaka-mai-wuya

Samin kwanciyar hankali

A lokacin da mace ta yi aure za a ga cewa akwai wata kwanciyar hankali na musamman da za ta fuskanta wanda duk inda ta je ba za ta same ta ba sai a gidan miji ire-iren wannan sauyi sun hada da amarci, soyayya, sannan kuma cima mai kyau, wadannan abubuwa suna da matukar tasiri a canjin halittar mace, cikin kankanin lokaci za a ga mace ta murmure ta murje.

Sabuwar Rayuwa da kuma samun ‘yancin kai

Bayan soyayya a aure akwai kuma wasu tarin nauyi da zai hau kan mace wanda hakan kansa ta fahimci cewar girma da kulawar wasu mutane ya hau kanta kamar su rainon ciki, haihuwa da kuma renon yaron da za ta haifa. Wannan sauyin da kwanciyar hankali suma suna kara taimaka wa mace wajen zama babbar mata. Sai a ga cikin kankanin lokaci mace ta murje ta yi jiki duk wasu jijiyoyi, kasusuwa, da kuma kwayar halittunta sun sami sauyi sun bude wanda hakan zai sa alamar kiba ta bayyana.

Rainon Ciki

Bayan hidimar aure akwai babbar hidima a gaban ma’aurata, wannan hidima ita ce daukar ciki. Haihuwa da aba ce mai matukar dadi da sa farin ciki kuma tana daga cikin abubuwa mafi sauki da ke kara wa mata budewar jiki ka ga sun yi kiba.

Daga lokacin da mace ta sami ciki to tabbas cin abincinta zai karu fiye da na da, za a ga idan a da tana cin karamin kwano to daga ta sami ciki sai ka ga abin ya canza, dole a nemo babban mazubi.

Mata yayin da suke da ciki suna matukar yin ciye-ciye sosai musamman abubuwa masu maiko wanda hakan ke sa jikin mace ya bude har ta yi jiki ta murmure.

Mata
Amina Usman
+ postsBio
  • Amina Usman
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-usman/
    Gasasshen Nama Mai Dankali
  • Amina Usman
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-usman/
    Shawara Ga Ma’aurata Game Da Hassada
  • Amina Usman
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-usman/
    Yadda Ake Miyar Zogale
  • Amina Usman
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-usman/
    Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

MASU ALAKA

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki
Nazari

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe
Manyan Labarai

Siyasar 2027: Yadda Ƴan Adawa Ke Ƙara Shiga Tsaka-mai-wuya

June 19, 2026
Lionel Messi: Mutum Ko Aljan
Wasanni

Lionel Messi: Mutum Ko Aljan

June 17, 2026
Next Post
Sin

Sin Za Ta Fadada Girman Tashar Binciken Samaniyarta

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.