• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Inganta NTA Ta Fara Gogayya Da Takwarorinta Na Duniya – Ministan Yada Labarai 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Za Mu Inganta NTA Ta Fara Gogayya Da Takwarorinta Na Duniya – Ministan Yada Labarai 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana aniyarsa ta ganin ya zamanantar da gidan talbijin ɗin Gwamnatin Tarayya (NTA) ta yadda zai yi goyayya da sauran manyan tashoshin talbijin da ake ji da su a duniya.

Idris ya ce zai ɗora kan shirin maida NTA bisa tsarin aiki cikin sauƙi kuma a zamanance, wato ‘Digital Switch Over’, wanda Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talbijin ta Ƙasa (NBC) ke kan yi.

  • Tsohon Minista Alhaji Bello Maitama Yusuf Ya Rasu Yana Da Shekaru 76 A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Muhimmanta ‘Yancin ‘Yan Jarida – Minista

Ministan ya yi wannan albishir ne a lokacin da ya kai ziyara a hedikwatar NTA, a wani rangadin duba hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar sa da ya ke yi, a ranar Talata.

Ya ce: “Dukkan mu dai mun san irin rawar da NTA ta taka da kuma gudunmawar ta wajen isar da saƙwanni da nishaɗantarwa ga ƙasar mu tsawon shekaru da dama. NTA ta na kan gaba wajen sanar da labarai da ɗumi-ɗumi masu muhimmanci ga ƙasa, sannan ta shahara wajen nuna kyawawan al’adun mu daga ɓangarorin ƙabilun ƙasar nan daban-daban.”

Ya yi tsinkayen cewa aikin babbar kafar yaɗa labarai kamar NTA abu ne da ya zama hantsi leƙa gidan kowa. Kan haka ne ya jinjina wa tashar dangane da yadda su ke gabatar da sahihan labarai, waɗanda ya ce sun taimaka sosai wajen isar da kyawawa kuma ingantattun bayanai ga ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Minista ya ƙara da cewa batun wayar da kan jama’a shi ne babban ginshiƙin da zai ƙarfafa ma’aikatar sa. Kan haka ne ya ce NTA za ta taka muhimmiyar rawa wajen yaɗa kyawawan ɗabi’un wayar da kan jama’a, waɗanda ma’aikatar sa za ta bijiro da su domin ɗora ƙasar nan kan nagartacciyar turbar cigaba mai ɗorewa.

Idris ya ce ya na fatan ganin ya bunƙasa NTA wadda ko bayan saukar sa daga mulki ya kasance ta na goyayya kafaɗa da kafaɗa da manyan gidajen talbijin ɗin da ake tinƙaho da su a duniya yanzu haka a ƙarni na 21.

Ya kuma yi alƙawarin zai samar wa NTA da dukkan kuɗaɗen da ta ke buƙata domin ganin cewa ayyukan ta na tafiya daidai, ba tare da tsaiko ko wata tangarɗa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NTANUJ
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Da Saudiyya Sun Yi Kunnen Doki A Wasan Sada Zumunta

Next Post

Sin Da Saudiyya Na Hadin Gwiwar Gina Sabon Birnin Red Sea Karkashin Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

Related

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
Manyan Labarai

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

40 minutes ago
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

2 hours ago
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
Manyan Labarai

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

3 hours ago
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 
Labarai

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

4 hours ago
UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 
Labarai

UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

4 hours ago
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja
Manyan Labarai

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

6 hours ago
Next Post
Sin Da Saudiyya Na Hadin Gwiwar Gina Sabon Birnin Red Sea Karkashin Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

Sin Da Saudiyya Na Hadin Gwiwar Gina Sabon Birnin Red Sea Karkashin Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

August 10, 2025
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

August 10, 2025
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.