• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Sha Alwashin Magance Talauci Da Kashi 80 Cikin 100 A Jihata – Gwamnan Kaduna

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Kaduna ta bada tabbacin hada hannu da malaman addini domin magance kalubalen talauci da ake fuskanta na sama da kashi 80 cikin 100 a yankunan karkara, za kuma ta mayar da yaran da basu zuwa makaranta ajujuwa domin samun zaman lafiya da cigaba a fadin jihar.

Gwamnan jihar, Malam Uba Sani ne ya bayyana hakan a yayin wani taro da kwamitin addini na jihar Kaduna, domin inganta zaman lafiya da inganta tsaro da aka gudanar a Kaduna.

  • Tinubu Ya Naɗa Sababbin Shugabannin Hukumomin Yaɗa Labarai
  • Gwamnatin Kaduna Ta Ware Naira Biliyan 3.1 Don Biyan Kuɗin Giratuti

Gwamna Sani ya roki malaman addinin Musulunci da na Kirista da su tallafawa gwamnati ta hanyar wa’azin wanzar da zaman lafiya a tsakanin mabiyansu.

Ya ce, ba za a iya samun zaman lafiya da tsaro a jihar ba, matukar kashi 80 cikin 100 na ‘yan jihar, musamman a yankunan karkara na fama da matsanancin talauci.

A cewarsa, akwai yara sama da 600,000 da ba sa zuwa makaranta a jihar, don haka, ya zama dole ne a mayar da su makaranta domin samun zaman lafiya a jihar.

Labarai Masu Nasaba

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

“Muna fuskantar matsaloli na fama da matsanancin talauci musamman a yankunan karkara. Kashi 80 cikin 100 na mutanen karkara na fama da matsanancin talauci. Wannan shi ne Gaskiyar magana.

“A watan da ya gabata, mun fara aikin gina tituna 32 a fadin jihar, wadanda akasarinsu na yankunan karkara ne.”

Gwamna Uba Sani ya kuma bayyana cewa, daga mako mai zuwa, gwamnatin jihar Kaduna za ta fara gina makarantu 100 domin mayar da yaran da ba sa zuwa makaranta ajujuwa domin magance matsalar rashin zuwa makaranta.

“An bar yara ba sa zuwa makaranta, suna yawo a kan tituna kuma a ce ana son a magance matsalar rashin tsaro? Ba zai yi wu ba. Don haka, dole ne a mayar da su makaranta.

“Bincikenmu ya nuna cewa, saboda talauci ne yawancin yaran ba su zuwa makaranta. Mutanen karkara ba sa tura ‘ya’yansu makaranta domin suna son su je gona ko kuma su tafi talla. Don haka, idan ba mu rage talauci daga kashi 80 cikin 100 zuwa akalla kashi 30 cikin 100 nan da shekaru masu zuwa ba, ba za mu taba iya magance matsalar yaran da ba su zuwa makaranta.”

Gwamnan ya jaddada cewa, dole ne gwamnatin ta farfado da tattalin arzikin yankunan karkara ta hanyar samar da ayyukan yi domin kawo karshen talauci.

Malam Uba Sani ya kuma bayyana cewa, gwamnatin Kaduna za ta hada kai da malaman addini wajen samar da bayanan marayu 5,000 a jihar domin basu tallafin karatu da gidauniyar tallafi ta Qatar ke daukar nauyi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin KadunaKalubalen rashin zuwa makarantaTalauci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kafa Kyakkyawan Misali A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama

Next Post

Dage Takunkumin Canjin Dala Ga Masu Shigo Da Kaya 43 A Sikeli

Related

Kawayen amarya
Manyan Labarai

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

2 hours ago
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
Labarai

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

3 hours ago
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri
Labarai

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

6 hours ago
EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
Manyan Labarai

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

7 hours ago
Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
Labarai

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

8 hours ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

9 hours ago
Next Post
dala

Dage Takunkumin Canjin Dala Ga Masu Shigo Da Kaya 43 A Sikeli

LABARAI MASU NASABA

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

June 18, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

June 18, 2025
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

June 18, 2025
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

June 18, 2025
“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

June 18, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.