• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas, James Ya Samu Lambar Kan Hidimta Wa Al’umma

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas, James Ya Samu Lambar Kan Hidimta Wa Al’umma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar Gudanar Da Harkokin Kasuwanci (ICA) ta karrama Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta kasa (NIS) a Jihar Ribas, James Sunday, bisa nuna kwazo, kwarewa da jajircewa wajen bayar da gagarumar gudunmawa a bangaren hidimta wa jama’a.

Wannan matakin na karamci da Mr James ya samu ya kai shi ga zama babban mambar cibiyar wacce aka lika masa alamin FCAI a cikin jerin sunansa.

A wata sanarwa dauke da sanya hannun Nwosu Chukwu, jami’in watsa labarai na NIS a jihar Ribas da ya fitar a ranar Asabar, ya kara da cewa an bada lambar yabon ne domin kara wa Kwanturolan azama a bangaren hidimta wa al’umma.

Shugaban reshen cibiyar ICA a jihar Ribas, Eze Sam Ubi Onyeka, wanda kuma shi ne daraktan gudanarwa a ma’aikatar yada labarai ta Fatakwal, ya mika wa James Sunday shaidar karramawar a wani kasaitaccen bikin da ya gudana.

  • Bai Kamata Shugaban Kasa Ya Nada Shugaban INEC Ba – Jega

 

Labarai Masu Nasaba

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Taron wanda ya samu halartar fitattun mutane da suka kunshi jami’an gudanarwa, daraktocin kamfanoni, jami’o’i da sauran cibiyoyin ilimi da suke jihar wadanda aka karrama bisa nuna godiya ga irin gudunmawar da suke bayarwa da kuma kamfanoni da suke gudanar da ayyuka na ci gaban al’umma da kuma sashin harkokin ilimi.

A wasikar da aka yi masa wacce ke alamta ba shi lambar yabon mai dauke da sanya hannun darakta kuma babban jami’in ilimi, Dakta Godswill C. Onyekwere, mai taken ‘Karramawa bisa gudunmawa ta kwarewa da gogewa a bangaren hidimta wa jama’a’.

“Wannan karamcin an ba ka ne domin nuna yabawa kan sadaukawa da kuma jajircewa wajen gudanar da aikin hidima wa jama’a tare da sanya kwarewa da kake yi wajen shawo kan lamura hadi da hangen nesa da kake da shi kan lamura.” In ji sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan matakin ya kai ka ga zama babban mambar cibiyar wanda aka lika maka shaidar FCAI a jikin sunanka. Muna taya ka murna da samun wannan babbar damar, muna maka fatan alkairi a tsawon shekarun da za ka shafe kana gudanar da aiki,” cibiyar ta sanar.

A jawabinsa na godiya, Kwanturola James Sunday, ya ce, wannan matakin lada ne ga irin aiki tukuru, sadaukar da kai, rashin son kai domin gudanar da aiki na kwarai, inda ya ce, “Wannan karamcin zai kara min kumaji wajen cigaba da yin aiki sosai domin al’umma.

“Abin a fayyace yake mutane suna nazarta kuma suna kallon ayyukan da muke gudanarwa, yana da kyau a kowani lokaci mutum ya zama mai yin aiki bisa cancanta.”

Ya misalta kyautar da ya samu a matsayin ni’ima daga Allah, sai ya sadaukar da ita ga jami’ansa, iyalansa bisa kwarin guiwar da suke ba shi a kowani lokaci da har ya iya cimma nasarori a rayuwarsa.

James ya karfafi sauran jami’ai da su kasance masu gudanar da ayyukansu bisa cancanta da nagarta hadi da gaskiya domin cigaban al’umma da kasa baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KarramawaRibaTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Kama Barayin Mota 3 A Bauchi

Next Post

NNPCL Ya Gargadi Masu Ɓoye Fetur Don Tsoron Ƙarin Farashin Man Da Samun Ƙarancinsa

Related

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

32 minutes ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

3 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

4 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

12 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

16 hours ago
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo
Labarai

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

18 hours ago
Next Post
NNPCL Ya Gargadi Masu Ɓoye Fetur Don Tsoron Ƙarin Farashin Man Da Samun Ƙarancinsa

NNPCL Ya Gargadi Masu Ɓoye Fetur Don Tsoron Ƙarin Farashin Man Da Samun Ƙarancinsa

LABARAI MASU NASABA

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.