• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas, James Ya Samu Lambar Kan Hidimta Wa Al’umma

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas, James Ya Samu Lambar Kan Hidimta Wa Al’umma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar Gudanar Da Harkokin Kasuwanci (ICA) ta karrama Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta kasa (NIS) a Jihar Ribas, James Sunday, bisa nuna kwazo, kwarewa da jajircewa wajen bayar da gagarumar gudunmawa a bangaren hidimta wa jama’a.

Wannan matakin na karamci da Mr James ya samu ya kai shi ga zama babban mambar cibiyar wacce aka lika masa alamin FCAI a cikin jerin sunansa.

A wata sanarwa dauke da sanya hannun Nwosu Chukwu, jami’in watsa labarai na NIS a jihar Ribas da ya fitar a ranar Asabar, ya kara da cewa an bada lambar yabon ne domin kara wa Kwanturolan azama a bangaren hidimta wa al’umma.

Shugaban reshen cibiyar ICA a jihar Ribas, Eze Sam Ubi Onyeka, wanda kuma shi ne daraktan gudanarwa a ma’aikatar yada labarai ta Fatakwal, ya mika wa James Sunday shaidar karramawar a wani kasaitaccen bikin da ya gudana.

  • Bai Kamata Shugaban Kasa Ya Nada Shugaban INEC Ba – Jega

 

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

Taron wanda ya samu halartar fitattun mutane da suka kunshi jami’an gudanarwa, daraktocin kamfanoni, jami’o’i da sauran cibiyoyin ilimi da suke jihar wadanda aka karrama bisa nuna godiya ga irin gudunmawar da suke bayarwa da kuma kamfanoni da suke gudanar da ayyuka na ci gaban al’umma da kuma sashin harkokin ilimi.

A wasikar da aka yi masa wacce ke alamta ba shi lambar yabon mai dauke da sanya hannun darakta kuma babban jami’in ilimi, Dakta Godswill C. Onyekwere, mai taken ‘Karramawa bisa gudunmawa ta kwarewa da gogewa a bangaren hidimta wa jama’a’.

“Wannan karamcin an ba ka ne domin nuna yabawa kan sadaukawa da kuma jajircewa wajen gudanar da aikin hidima wa jama’a tare da sanya kwarewa da kake yi wajen shawo kan lamura hadi da hangen nesa da kake da shi kan lamura.” In ji sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan matakin ya kai ka ga zama babban mambar cibiyar wanda aka lika maka shaidar FCAI a jikin sunanka. Muna taya ka murna da samun wannan babbar damar, muna maka fatan alkairi a tsawon shekarun da za ka shafe kana gudanar da aiki,” cibiyar ta sanar.

A jawabinsa na godiya, Kwanturola James Sunday, ya ce, wannan matakin lada ne ga irin aiki tukuru, sadaukar da kai, rashin son kai domin gudanar da aiki na kwarai, inda ya ce, “Wannan karamcin zai kara min kumaji wajen cigaba da yin aiki sosai domin al’umma.

“Abin a fayyace yake mutane suna nazarta kuma suna kallon ayyukan da muke gudanarwa, yana da kyau a kowani lokaci mutum ya zama mai yin aiki bisa cancanta.”

Ya misalta kyautar da ya samu a matsayin ni’ima daga Allah, sai ya sadaukar da ita ga jami’ansa, iyalansa bisa kwarin guiwar da suke ba shi a kowani lokaci da har ya iya cimma nasarori a rayuwarsa.

James ya karfafi sauran jami’ai da su kasance masu gudanar da ayyukansu bisa cancanta da nagarta hadi da gaskiya domin cigaban al’umma da kasa baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KarramawaRibaTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Kama Barayin Mota 3 A Bauchi

Next Post

NNPCL Ya Gargadi Masu Ɓoye Fetur Don Tsoron Ƙarin Farashin Man Da Samun Ƙarancinsa

Related

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi
Labarai

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

44 minutes ago
AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate
Ilimi

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

1 hour ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

13 hours ago
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

15 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

16 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

19 hours ago
Next Post
NNPCL Ya Gargadi Masu Ɓoye Fetur Don Tsoron Ƙarin Farashin Man Da Samun Ƙarancinsa

NNPCL Ya Gargadi Masu Ɓoye Fetur Don Tsoron Ƙarin Farashin Man Da Samun Ƙarancinsa

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

July 7, 2025
AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

July 7, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.