ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas, James Ya Samu Lambar Kan Hidimta Wa Al’umma

by Khalid Idris Doya
3 years ago
James

Cibiyar Gudanar Da Harkokin Kasuwanci (ICA) ta karrama Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta kasa (NIS) a Jihar Ribas, James Sunday, bisa nuna kwazo, kwarewa da jajircewa wajen bayar da gagarumar gudunmawa a bangaren hidimta wa jama’a.

Wannan matakin na karamci da Mr James ya samu ya kai shi ga zama babban mambar cibiyar wacce aka lika masa alamin FCAI a cikin jerin sunansa.

A wata sanarwa dauke da sanya hannun Nwosu Chukwu, jami’in watsa labarai na NIS a jihar Ribas da ya fitar a ranar Asabar, ya kara da cewa an bada lambar yabon ne domin kara wa Kwanturolan azama a bangaren hidimta wa al’umma.

ADVERTISEMENT

Shugaban reshen cibiyar ICA a jihar Ribas, Eze Sam Ubi Onyeka, wanda kuma shi ne daraktan gudanarwa a ma’aikatar yada labarai ta Fatakwal, ya mika wa James Sunday shaidar karramawar a wani kasaitaccen bikin da ya gudana.

  • Bai Kamata Shugaban Kasa Ya Nada Shugaban INEC Ba – Jega

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Taron wanda ya samu halartar fitattun mutane da suka kunshi jami’an gudanarwa, daraktocin kamfanoni, jami’o’i da sauran cibiyoyin ilimi da suke jihar wadanda aka karrama bisa nuna godiya ga irin gudunmawar da suke bayarwa da kuma kamfanoni da suke gudanar da ayyuka na ci gaban al’umma da kuma sashin harkokin ilimi.

A wasikar da aka yi masa wacce ke alamta ba shi lambar yabon mai dauke da sanya hannun darakta kuma babban jami’in ilimi, Dakta Godswill C. Onyekwere, mai taken ‘Karramawa bisa gudunmawa ta kwarewa da gogewa a bangaren hidimta wa jama’a’.

“Wannan karamcin an ba ka ne domin nuna yabawa kan sadaukawa da kuma jajircewa wajen gudanar da aikin hidima wa jama’a tare da sanya kwarewa da kake yi wajen shawo kan lamura hadi da hangen nesa da kake da shi kan lamura.” In ji sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan matakin ya kai ka ga zama babban mambar cibiyar wanda aka lika maka shaidar FCAI a jikin sunanka. Muna taya ka murna da samun wannan babbar damar, muna maka fatan alkairi a tsawon shekarun da za ka shafe kana gudanar da aiki,” cibiyar ta sanar.

A jawabinsa na godiya, Kwanturola James Sunday, ya ce, wannan matakin lada ne ga irin aiki tukuru, sadaukar da kai, rashin son kai domin gudanar da aiki na kwarai, inda ya ce, “Wannan karamcin zai kara min kumaji wajen cigaba da yin aiki sosai domin al’umma.

“Abin a fayyace yake mutane suna nazarta kuma suna kallon ayyukan da muke gudanarwa, yana da kyau a kowani lokaci mutum ya zama mai yin aiki bisa cancanta.”

Ya misalta kyautar da ya samu a matsayin ni’ima daga Allah, sai ya sadaukar da ita ga jami’ansa, iyalansa bisa kwarin guiwar da suke ba shi a kowani lokaci da har ya iya cimma nasarori a rayuwarsa.

James ya karfafi sauran jami’ai da su kasance masu gudanar da ayyukansu bisa cancanta da nagarta hadi da gaskiya domin cigaban al’umma da kasa baki daya.

James
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
NNPCL Ya Gargadi Masu Ɓoye Fetur Don Tsoron Ƙarin Farashin Man Da Samun Ƙarancinsa

NNPCL Ya Gargadi Masu Ɓoye Fetur Don Tsoron Ƙarin Farashin Man Da Samun Ƙarancinsa

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.