ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas, James Ya Samu Lambar Kan Hidimta Wa Al’umma

by Khalid Idris Doya
3 years ago
James

Cibiyar Gudanar Da Harkokin Kasuwanci (ICA) ta karrama Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta kasa (NIS) a Jihar Ribas, James Sunday, bisa nuna kwazo, kwarewa da jajircewa wajen bayar da gagarumar gudunmawa a bangaren hidimta wa jama’a.

Wannan matakin na karamci da Mr James ya samu ya kai shi ga zama babban mambar cibiyar wacce aka lika masa alamin FCAI a cikin jerin sunansa.

A wata sanarwa dauke da sanya hannun Nwosu Chukwu, jami’in watsa labarai na NIS a jihar Ribas da ya fitar a ranar Asabar, ya kara da cewa an bada lambar yabon ne domin kara wa Kwanturolan azama a bangaren hidimta wa al’umma.

ADVERTISEMENT

Shugaban reshen cibiyar ICA a jihar Ribas, Eze Sam Ubi Onyeka, wanda kuma shi ne daraktan gudanarwa a ma’aikatar yada labarai ta Fatakwal, ya mika wa James Sunday shaidar karramawar a wani kasaitaccen bikin da ya gudana.

  • Bai Kamata Shugaban Kasa Ya Nada Shugaban INEC Ba – Jega

 

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Taron wanda ya samu halartar fitattun mutane da suka kunshi jami’an gudanarwa, daraktocin kamfanoni, jami’o’i da sauran cibiyoyin ilimi da suke jihar wadanda aka karrama bisa nuna godiya ga irin gudunmawar da suke bayarwa da kuma kamfanoni da suke gudanar da ayyuka na ci gaban al’umma da kuma sashin harkokin ilimi.

A wasikar da aka yi masa wacce ke alamta ba shi lambar yabon mai dauke da sanya hannun darakta kuma babban jami’in ilimi, Dakta Godswill C. Onyekwere, mai taken ‘Karramawa bisa gudunmawa ta kwarewa da gogewa a bangaren hidimta wa jama’a’.

“Wannan karamcin an ba ka ne domin nuna yabawa kan sadaukawa da kuma jajircewa wajen gudanar da aikin hidima wa jama’a tare da sanya kwarewa da kake yi wajen shawo kan lamura hadi da hangen nesa da kake da shi kan lamura.” In ji sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan matakin ya kai ka ga zama babban mambar cibiyar wanda aka lika maka shaidar FCAI a jikin sunanka. Muna taya ka murna da samun wannan babbar damar, muna maka fatan alkairi a tsawon shekarun da za ka shafe kana gudanar da aiki,” cibiyar ta sanar.

A jawabinsa na godiya, Kwanturola James Sunday, ya ce, wannan matakin lada ne ga irin aiki tukuru, sadaukar da kai, rashin son kai domin gudanar da aiki na kwarai, inda ya ce, “Wannan karamcin zai kara min kumaji wajen cigaba da yin aiki sosai domin al’umma.

“Abin a fayyace yake mutane suna nazarta kuma suna kallon ayyukan da muke gudanarwa, yana da kyau a kowani lokaci mutum ya zama mai yin aiki bisa cancanta.”

Ya misalta kyautar da ya samu a matsayin ni’ima daga Allah, sai ya sadaukar da ita ga jami’ansa, iyalansa bisa kwarin guiwar da suke ba shi a kowani lokaci da har ya iya cimma nasarori a rayuwarsa.

James ya karfafi sauran jami’ai da su kasance masu gudanar da ayyukansu bisa cancanta da nagarta hadi da gaskiya domin cigaban al’umma da kasa baki daya.

James
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
NNPCL Ya Gargadi Masu Ɓoye Fetur Don Tsoron Ƙarin Farashin Man Da Samun Ƙarancinsa

NNPCL Ya Gargadi Masu Ɓoye Fetur Don Tsoron Ƙarin Farashin Man Da Samun Ƙarancinsa

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.