• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Fashin Daji Na Cin Karensu Ba Babbaka A Jihar Katsina

by Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani rahoto da BBC Hausa tawa wallafa yana cewa, Jama’a a ƙaramar hukumar Faskari ta jihar Katsina sun ce sun shiga tsaka mai wuya sakamakon yadda ‘yan bindiga suka mamaye garuruwansu, kuma suka mayar da su tamkar bayi.

Mazauna yankin sun ce ƴan bindigar sun kwace gonakin jama’a, tare da tilasta wa mutanen garuruwan yi masu shuka da huɗa da ma sauran ayyukan gona.

  • ‘Yan Fashin Daji Sun Kashe Kansila A Katsina
  • Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Fashin Daji Luguden Wuta, Sun Kashe 22 A Katsina

Yanzu haka dai jama’ar da ƴan bindigar suka mamaye a yankin ƙaramar hukumar Faskarin ta Nijeriya suna cikin ƙunci da damuwa.

Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunan sa ya shaidawa BBC cewa ƴan bindigar suna shiga ƙauyuka kuma su yi abin da suke so, kuma a lokacin da suke so.

Ya ce ‘‘A yanzu maganar da ake a cikin firamare din Kogo ƴan bindiga ne a ciki zaune, in an yi abinci a kai masu, in suka ga yarinya su ɗauka, in kuma ka yi magana su kashe ka.’’

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

Mutumin ya ce mazauna yankin suna biyayya ne ga ƴan bindigar saboda basu da wani zaɓi na daban.

‘‘tashin farko dai suka sa aka haɗa masu kuɗi cikin yarjejeniyar da aka yi, da kuma gonakin da suka ware waɗanna ba za a noma ba, su za a nomawa. Duk lokacin noma za mu je can, mu yi masu hu mu yi masu noma, mu yi masu huɗa, su faɗa mana abin da za a noma, mu yi noma kuma idan lokacin girbi ya yi mu kwashe mu basu. Sun maida mu tamkar bayi a cikin wannan yanki, idan ka yi kaifi a hukunta ka’’

Ya ce ƙauyukna yankin da suka haɗa da Birnin Kogo da Yar-tsamiya da Kahi da Fankama da Hayin Dungu da kuma Gobirawa duk ƙarƙashin ikon ƴan bindigar suke, waɗanda ke ci gaba da murgunawa jama’a.

Dr Nasir Mu’azu, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Katsina ya ce gwamnatin jihar ta farga da wannan lamari.

‘‘Mutane a irin waɗannan ƙauyuka sun je sansanin ƴan gudun hijira, to kuma wasu da yawa ba za su iya haƙuri da zaman sansanin ba don haka sai suka koma ƙauyukan su, suna ci gaba da zama bisa ga yadda ƴan bindigar suke ta gallaza masu’’

Dr Nasir ya ce gwamnan jihar Katsina Dikko Umar Radda yana aiki tuƙuru don kula da mutanen da matsalar tsaron ta tilasta masu yin hijira da kuma tabbatar da tsaro a faɗin jihar.

Gwamnatin jihar Katsina dai ta lashi takobin magance matsalar tsaro da ta dabaibaye garuruwa da ƙauyuka da dama na jihar. Kuma ko a kwanan nan sai da ta ƙaddamar da rundunar sintiri ta farar hula don taimakawa wajen tabbatar da tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Ci Gaba Da Alhinin Mutuwar Malam Adamu Fika

Next Post

Bayan Nasara A Kotun Ƙoli, Tinubu Zai Ci Gaba Da Aikin Gina Nagartacciyar Ƙasa – Minista

Related

Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

1 hour ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

4 hours ago
An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani
Manyan Labarai

An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani

8 hours ago
Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3
Manyan Labarai

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

10 hours ago
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Kasashen Ketare

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

11 hours ago
Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

18 hours ago
Next Post
Bayan Nasara A Kotun Ƙoli, Tinubu Zai Ci Gaba Da Aikin Gina Nagartacciyar Ƙasa – Minista

Bayan Nasara A Kotun Ƙoli, Tinubu Zai Ci Gaba Da Aikin Gina Nagartacciyar Ƙasa - Minista

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

June 24, 2025
Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

June 24, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

June 24, 2025
Shugaban CMG Ya Zanta Da Manyan Jami’an IOC

Shugaban CMG Ya Zanta Da Manyan Jami’an IOC

June 24, 2025
An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani

An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani

June 24, 2025
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

June 24, 2025
Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

June 24, 2025
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.