• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Fashin Daji Na Cin Karensu Ba Babbaka A Jihar Katsina

by Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani rahoto da BBC Hausa tawa wallafa yana cewa, Jama’a a ƙaramar hukumar Faskari ta jihar Katsina sun ce sun shiga tsaka mai wuya sakamakon yadda ‘yan bindiga suka mamaye garuruwansu, kuma suka mayar da su tamkar bayi.

Mazauna yankin sun ce ƴan bindigar sun kwace gonakin jama’a, tare da tilasta wa mutanen garuruwan yi masu shuka da huɗa da ma sauran ayyukan gona.

  • ‘Yan Fashin Daji Sun Kashe Kansila A Katsina
  • Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Fashin Daji Luguden Wuta, Sun Kashe 22 A Katsina

Yanzu haka dai jama’ar da ƴan bindigar suka mamaye a yankin ƙaramar hukumar Faskarin ta Nijeriya suna cikin ƙunci da damuwa.

Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunan sa ya shaidawa BBC cewa ƴan bindigar suna shiga ƙauyuka kuma su yi abin da suke so, kuma a lokacin da suke so.

Ya ce ‘‘A yanzu maganar da ake a cikin firamare din Kogo ƴan bindiga ne a ciki zaune, in an yi abinci a kai masu, in suka ga yarinya su ɗauka, in kuma ka yi magana su kashe ka.’’

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Mutumin ya ce mazauna yankin suna biyayya ne ga ƴan bindigar saboda basu da wani zaɓi na daban.

‘‘tashin farko dai suka sa aka haɗa masu kuɗi cikin yarjejeniyar da aka yi, da kuma gonakin da suka ware waɗanna ba za a noma ba, su za a nomawa. Duk lokacin noma za mu je can, mu yi masu hu mu yi masu noma, mu yi masu huɗa, su faɗa mana abin da za a noma, mu yi noma kuma idan lokacin girbi ya yi mu kwashe mu basu. Sun maida mu tamkar bayi a cikin wannan yanki, idan ka yi kaifi a hukunta ka’’

Ya ce ƙauyukna yankin da suka haɗa da Birnin Kogo da Yar-tsamiya da Kahi da Fankama da Hayin Dungu da kuma Gobirawa duk ƙarƙashin ikon ƴan bindigar suke, waɗanda ke ci gaba da murgunawa jama’a.

Dr Nasir Mu’azu, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Katsina ya ce gwamnatin jihar ta farga da wannan lamari.

‘‘Mutane a irin waɗannan ƙauyuka sun je sansanin ƴan gudun hijira, to kuma wasu da yawa ba za su iya haƙuri da zaman sansanin ba don haka sai suka koma ƙauyukan su, suna ci gaba da zama bisa ga yadda ƴan bindigar suke ta gallaza masu’’

Dr Nasir ya ce gwamnan jihar Katsina Dikko Umar Radda yana aiki tuƙuru don kula da mutanen da matsalar tsaron ta tilasta masu yin hijira da kuma tabbatar da tsaro a faɗin jihar.

Gwamnatin jihar Katsina dai ta lashi takobin magance matsalar tsaro da ta dabaibaye garuruwa da ƙauyuka da dama na jihar. Kuma ko a kwanan nan sai da ta ƙaddamar da rundunar sintiri ta farar hula don taimakawa wajen tabbatar da tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Ci Gaba Da Alhinin Mutuwar Malam Adamu Fika

Next Post

Bayan Nasara A Kotun Ƙoli, Tinubu Zai Ci Gaba Da Aikin Gina Nagartacciyar Ƙasa – Minista

Related

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

4 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

4 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

5 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

6 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

7 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

8 hours ago
Next Post
Bayan Nasara A Kotun Ƙoli, Tinubu Zai Ci Gaba Da Aikin Gina Nagartacciyar Ƙasa – Minista

Bayan Nasara A Kotun Ƙoli, Tinubu Zai Ci Gaba Da Aikin Gina Nagartacciyar Ƙasa - Minista

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.