• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Diphtheria: Gwamnatin Kano Ta Yi Gargadi Kan Hada Taruka

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Diphtheria: Gwamnatin Kano Ta Yi Gargadi Kan Hada Taruka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan Lafiya na Jihar Kano, Dakta Abubakar Labaran Yusuf ya yi kira ga jama’a da su guji zuwa taruka da ba dole ba domin kare kansu da sauran jama’a daga kamuwa da cutar diphtheria.

Dakta Labaran ya yi wannan kiran ne a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Laraba.

  • Shirin Tsige Fubara: Gwamnonin PDP Za Su Gana Da Wike A Abuja
  • Hatsarin Kwale-Kwale: Har Yanzu Ana Neman Mutane Sama Da 70 A Taraba – NEMA

A cewarsa, ya zama wajibi wajen wayar da kan jama’a kan wajibcin daukar matakan kariya da nufin dakile yaduwar cutar diphtheria a jihar Kano.

Kwamishinan ya ce cutar diphtheria cuta ce da ke yaduwa ta iska, don haka duk mutumin da ake zargin ya kamu da cutar ko kuma yake dauke da alamun cutar da su ziyarci likita don duba su.

Ya jaddada cewa a guji cudanya ta hanyar musabaha ko atishawa da mutane masu dauke da alamun cutar, inda ya bayyana cewa wadannan su ne manyan hanyoyin yada cutar.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Dakta Labaran ya ba da shawarar cewa idan yaro ne ya kamu da cutar, kada iyaye su bari ya je makaranta su gaggauta kai shi asibiti don yi masa gwaje-gwaje da duba lafiyarsa.

Kwamishinan ya gargadi mutane da su daina hada taruka marasa amfani musamman ganin yadda lokacin sanyi ke karatowa, lamarin da ka iya ta’azzara cutar diphtheria.

Ya kara da cewa idan taro ya zama wajibi, to ya kamata a yi a waje mai ishasshiyar iska.

Dokta Labaran ya bayyana cewa, babbar hanyar kariya daga cutar diphtheria ita ce allurar rigakafi, ya kuma yi kira ga iyaye da su tabbatar da an yi wa ‘ya’yansu masu shekaru hudu zuwa 14 rigakafin sau uku a jere, domin kare su daga kamuwa daga cutar.

Har wa yau ya bayyana cewa idan yaro ya kamu da cutar amai da gudawa, dole ne a yi wa dukkan ‘yan uwansa allurar rigakafi don kare shi daga diphtheria da kuma wasu cututtuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CutaDiphtheriaGargadigwamnatikano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-yanzu: ‘Yansanda Sun Cafke Shugaban NLC, Joe Ajaero A Imo

Next Post

Kotun Daukaka Kara Ta Tsige Suswam Daga Kujerar Sanata 

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

1 hour ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

13 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

18 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

19 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da ÆŠansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

20 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da ÆŠansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

21 hours ago
Next Post
Suswam

Kotun Daukaka Kara Ta Tsige Suswam Daga Kujerar Sanata 

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.