ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hatsarin Kwale-Kwale: Har Yanzu Ana Neman Mutane Sama Da 70 A Taraba – NEMA

by Sadiq
3 years ago
NEMA

Ya zuwa yanzu hukumomi a Jihar Taraba sun tabbatar da mutuwar mutum 17 yayin da aka ceto mutum 14.

Kwale-kwalen da ya yi hatsari na dauke da ‘yan kasuwa da ke dawowa daga kasuwar kifi da ke gundumar Ardo-Kola ta jihar Taraba da yammacin ranar Asabar lokacin da ya kife a Kogin Benue, wanda shi ne daya daga cikin ruwa mafi girma a Nijeriya.

  • Gwamna Lawal Ya Jagoranci Taron Majalisar Zartaswa Kan Tattara Kudin Fansho
  • ‘Yansanda Sun Cafke Saurayin Budurwar Da Ta Mutu Yayin Jima’i A Kwara

Fiye da fasinjoji 100 ne ke cikin jirgin, sannan an ceto 14, yayin da aka gano gawarwaki mutane 17, amma kuma mutane 73 ne suka bace, kamar yadda shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, Ladan Ayuba, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN).

ADVERTISEMENT

Gwamnan jihar Taraba Agbu Kefas ya kwatanta hatsarin a matsayin babban abin takaici kuma ya ba da umarnin amfani da rigunan ceto ga fasinjojin kwale-kwale.

“Ruwan kasarmu, wanda shi ne daya daga cikin mafi dadewa a yankin, ya kamata ya zama tushen arziki ne ba na mutuwa ba,” in ji gwamnan, a cewar wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Iftila’in kifewar kwale-kwale na kara zama ruwan dare a tsakanin al’ummomi da ke yankunan karkara a a wasu jihohin Nijeriya.

Wannan shi ne hatsari na uku da ya shafi fasinjoji sama da 100 cikin watanni hudu kacal.

Yawanci ana danganta haduran da daukar kaya fiye da kima.

Babu hanyoyin mota masu inganci a ire-iren wadannan yankuna.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Taraba, Usman Abdullahi ya ce jami’an tsaro na gudanar da bincike don gano musabbabin faruwar wannan hatsarin.

Mazauna yankin da masunta suna taimaka wa hukumomin ceto don ganin an kubutar da wadanda lamarin ya rutsa da su.

Abdullahi ya ce yana fargabar cewa aikin binciken na iya daukar kwanaki kafin a kammala saboda kogin yana kan ganiyar tumbatsa.

“Ba ma tsammanin za mu samu gawarwakin a nan kusa,” in ji shi.

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Tattalin Arzikin Kasashen Afirka Zai Dade Bai Farfado Ba – AFDB

Tattalin Arzikin Kasashen Afirka Zai Dade Bai Farfado Ba - AFDB

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.