ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hatsarin Kwale-Kwale: Har Yanzu Ana Neman Mutane Sama Da 70 A Taraba – NEMA

by Sadiq
3 years ago
NEMA

Ya zuwa yanzu hukumomi a Jihar Taraba sun tabbatar da mutuwar mutum 17 yayin da aka ceto mutum 14.

Kwale-kwalen da ya yi hatsari na dauke da ‘yan kasuwa da ke dawowa daga kasuwar kifi da ke gundumar Ardo-Kola ta jihar Taraba da yammacin ranar Asabar lokacin da ya kife a Kogin Benue, wanda shi ne daya daga cikin ruwa mafi girma a Nijeriya.

  • Gwamna Lawal Ya Jagoranci Taron Majalisar Zartaswa Kan Tattara Kudin Fansho
  • ‘Yansanda Sun Cafke Saurayin Budurwar Da Ta Mutu Yayin Jima’i A Kwara

Fiye da fasinjoji 100 ne ke cikin jirgin, sannan an ceto 14, yayin da aka gano gawarwaki mutane 17, amma kuma mutane 73 ne suka bace, kamar yadda shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, Ladan Ayuba, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN).

ADVERTISEMENT

Gwamnan jihar Taraba Agbu Kefas ya kwatanta hatsarin a matsayin babban abin takaici kuma ya ba da umarnin amfani da rigunan ceto ga fasinjojin kwale-kwale.

“Ruwan kasarmu, wanda shi ne daya daga cikin mafi dadewa a yankin, ya kamata ya zama tushen arziki ne ba na mutuwa ba,” in ji gwamnan, a cewar wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Iftila’in kifewar kwale-kwale na kara zama ruwan dare a tsakanin al’ummomi da ke yankunan karkara a a wasu jihohin Nijeriya.

Wannan shi ne hatsari na uku da ya shafi fasinjoji sama da 100 cikin watanni hudu kacal.

Yawanci ana danganta haduran da daukar kaya fiye da kima.

Babu hanyoyin mota masu inganci a ire-iren wadannan yankuna.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Taraba, Usman Abdullahi ya ce jami’an tsaro na gudanar da bincike don gano musabbabin faruwar wannan hatsarin.

Mazauna yankin da masunta suna taimaka wa hukumomin ceto don ganin an kubutar da wadanda lamarin ya rutsa da su.

Abdullahi ya ce yana fargabar cewa aikin binciken na iya daukar kwanaki kafin a kammala saboda kogin yana kan ganiyar tumbatsa.

“Ba ma tsammanin za mu samu gawarwakin a nan kusa,” in ji shi.

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Tattalin Arzikin Kasashen Afirka Zai Dade Bai Farfado Ba – AFDB

Tattalin Arzikin Kasashen Afirka Zai Dade Bai Farfado Ba - AFDB

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.