ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Tsige Fubara: Gwamnonin PDP Za Su Gana Da Wike A Abuja

by Sadiq
3 years ago
PDP

Gwamnonin jam’iyyar PDP za su gana da ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike, kan halin da ake ciki a Jihar Ribas, yayin da ake neman tsige gwamnan Jihar, Siminalayi Fubara.

Darakta Janar na kungiyar gwamnonin PDP, CID Maduabum, ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar bayan taron kungiyar a ranar Talata.

  • Malaman Makaranta 1,700 Sun Koka Kan Rashin Biyan Su Albashin Shekaru 3 
  • CBN Ya Rufe Wasu Bankuna 754 Sakamakon Shiga Matsaloli

Gwamnonin za su gana da ministan a yau Laraba a ofishinsa.

ADVERTISEMENT

Shugaban kungiyar, Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi, ne zai jagoranci wasu gwamnoni kusan 10 na jam’iyyar PDP zuwa ofishin ministan babban birnin tarayya Abuja domin tattaunawa.

“Bayan shawarar da aka cimma a taron kungiyar gwamnonin PDP a ranar Talata, 31 ga watan Oktoba, za mu ziyarci Ministan babban birnin tarayya Abuja, domin sasanci,” in ji sanarwar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Kungiyar ta yi taro ne a ranar Talata inda ta bukaci ‘yan siyasa a Kudu-maso-Kudu da su yi wani abu don warware rikicin cikin ruwan sanyi.

Wadanda suka halarci taron sun hada da: Gwamna Bala Mohammed (Bauchi), Gwamna Ahmadu Fintiri (Adamawa), Gwamna Sheriff Oborevwori (Delta), Gwamna Ademola Adeleke (Osun), Gwamna Seyi Makinde (Oyo), Gwamna Caleb Mutfwang (Filato), Gwamna Godwin Obaseki. (Edo), Gwamna Kefas Agbu (Taraba), Gwamna Dauda Lawal (Zamfara), Gwamna Siminalayi Fubara (Ribas) da Mataimakin Gwamna Ifeanyi Ossai (Enugu).

A wajen taron, gwamnonin PDP sun yi maraba da shiga tsakani da shugaba Bola Tinubu ya yi ta hanyar ganawa da Fubara da Wike a fadar Aso Villa da ke Abuja da yammacin ranar Talata domin warware rikicin.

Ganawar da shugaban kasar ya yi da ‘yan siyasar biyu na PDP ya biyo bayan yunkurin tsige Fubara da majalisar dokokin jihar Ribas ta yi a ranar Litinin.

Majalisar dokokin jihar ta zargi gwamnan da aikata munanan ayyukan da ba su dace ba a matsayinsa na gwamna.

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

Yanzu-yanzu: 'Yansanda Sun Cafke Shugaban NLC, Joe Ajaero A Imo

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.