ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Tsige Fubara: Gwamnonin PDP Za Su Gana Da Wike A Abuja

by Sadiq
3 years ago
PDP

Gwamnonin jam’iyyar PDP za su gana da ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike, kan halin da ake ciki a Jihar Ribas, yayin da ake neman tsige gwamnan Jihar, Siminalayi Fubara.

Darakta Janar na kungiyar gwamnonin PDP, CID Maduabum, ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar bayan taron kungiyar a ranar Talata.

  • Malaman Makaranta 1,700 Sun Koka Kan Rashin Biyan Su Albashin Shekaru 3 
  • CBN Ya Rufe Wasu Bankuna 754 Sakamakon Shiga Matsaloli

Gwamnonin za su gana da ministan a yau Laraba a ofishinsa.

ADVERTISEMENT

Shugaban kungiyar, Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi, ne zai jagoranci wasu gwamnoni kusan 10 na jam’iyyar PDP zuwa ofishin ministan babban birnin tarayya Abuja domin tattaunawa.

“Bayan shawarar da aka cimma a taron kungiyar gwamnonin PDP a ranar Talata, 31 ga watan Oktoba, za mu ziyarci Ministan babban birnin tarayya Abuja, domin sasanci,” in ji sanarwar.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Kungiyar ta yi taro ne a ranar Talata inda ta bukaci ‘yan siyasa a Kudu-maso-Kudu da su yi wani abu don warware rikicin cikin ruwan sanyi.

Wadanda suka halarci taron sun hada da: Gwamna Bala Mohammed (Bauchi), Gwamna Ahmadu Fintiri (Adamawa), Gwamna Sheriff Oborevwori (Delta), Gwamna Ademola Adeleke (Osun), Gwamna Seyi Makinde (Oyo), Gwamna Caleb Mutfwang (Filato), Gwamna Godwin Obaseki. (Edo), Gwamna Kefas Agbu (Taraba), Gwamna Dauda Lawal (Zamfara), Gwamna Siminalayi Fubara (Ribas) da Mataimakin Gwamna Ifeanyi Ossai (Enugu).

A wajen taron, gwamnonin PDP sun yi maraba da shiga tsakani da shugaba Bola Tinubu ya yi ta hanyar ganawa da Fubara da Wike a fadar Aso Villa da ke Abuja da yammacin ranar Talata domin warware rikicin.

Ganawar da shugaban kasar ya yi da ‘yan siyasar biyu na PDP ya biyo bayan yunkurin tsige Fubara da majalisar dokokin jihar Ribas ta yi a ranar Litinin.

Majalisar dokokin jihar ta zargi gwamnan da aikata munanan ayyukan da ba su dace ba a matsayinsa na gwamna.

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

Yanzu-yanzu: 'Yansanda Sun Cafke Shugaban NLC, Joe Ajaero A Imo

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.