• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CITAD Ta Horas Da Yan Mata Kan Fasahar Zamani

by Leadership Hausa
2 years ago
in Ilimi
0
CITAD Ta Horas Da Yan Mata Kan Fasahar Zamani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar Bunkasa Fasahar Sadarwa (CITAD), ta horas da yan mata ashirin da biyar da aka zakulo daga sassan Nijeriya kan yadda za su shiga a dama da su wajen fasahar sadarwar zamani da jagoranci.

Da take magana da yan jarida a yayin horon na kwanaki biyu da ya gudana a Bauchi makon jiya, jamiar kula da bangaren jinsi na CITAD, Zainab Aminu, ta ce, an zabo matan ne kuma an ba su horo na musamman a bangarorin shugabanci ta yadda za su shiga a dama da su a bangaren fasahar sadarwa tare da fuskantar kalubalen da mata ke fuskanta dangane da mu’amala da fasahar zamani.

  • CITAD Ta Bai Wa ‘Yan Jarida 10 Tallafi Don Gudanar Da Bincike Game Da Cin Hanci
  • Manyan Kalubalen Da Ke Durkusar Da Kiwon Kifi A Nijeriya

Ta ce, matan sun kuma samu horon yadda za su rungumi bangaren ICT domin shawo kan wariyar da ake yi wa mata a wannan fannin da kuma basu damar shiga a dama da su a bangaren fasahar sadarwa, hadi da tsare-tsaren da suka shafi kyautata harkokin jinsi.

Jamiar ta kara da cewa bangarorin da horon ya kuma maida hankali sun hada da tsare-tsaren fasahar sadarwa, matakan amfani da yanar gizo, hanyoyin da ake amfani da kafafen sadarwa ba tare da wani musgunawa ko cin zarafinsu ba, hadi da tsare-tsaren yadda za su samu damar kirkirar abubuwa tare da samar da damarmaki ga mata.

Zainab Aminu ta kara da cewa, lokaci ya yi da mata za su amfana da dukkanin damarmakin da ke cikin fasahar zamani ba tare da tsangwama ba.

Labarai Masu Nasaba

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

Wannan horaswar ta jagoranci na da manufar wayar da kan mata kan yadda za su samu damar shiga a dama da su kan tsare-tsare da yadda za su shiga a yi da su a bangaren ICT da kuma dabarun yadda za su samu ilimi kan sauye-sauye, ta shaida.

Ita ma da take magana, daraktan cibiyar kere-kere ta Bloom, Hannah Kabrang, ta ce, horaswar zai taimakesu wajen kara samun damarmakin yadda za su fuskanci tsare-tsaren fasahar sadarwa da kuma yadda za su taimaki mata su shiga a dama da su wajen amfanuwa da zamani.

Ita ma Sadiya Lawan, daliba a jamiar Dutsin-Ma, da ta kasance mahalarciyar taron, ta ce, sun samu gogewar yadda za su fuskanci kowani irin kalubalen da ke fuskantar mata a kafafen sadarwar zamani da kuma fasahar zamani gaba daya.

Tana mai cewa an kuma basu horon ta yadda su ma za su koyar da wasu yadda za su fuskanci wadannan matsalolin da mata ke fuskanta musamman a kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CitadFasahar Zamanikano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadarin Mota: NIS Ta Tabbatar Da Mutuwar Jamianta 4, 7 Sun Ji Rauni A Kano

Next Post

Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

Related

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

2 days ago
Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima
Ilimi

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

1 week ago
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah
Ilimi

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

3 weeks ago
Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya
Ilimi

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

3 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

1 month ago
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

1 month ago
Next Post
Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

LABARAI MASU NASABA

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.