• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Na Fatan A Tabbatar Da Daidaiton Da Aka Cimma A San Francisco

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Duniya Na Fatan A Tabbatar Da Daidaiton Da Aka Cimma A San Francisco
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka, duniyarmu na fuskantar manyan sauye-sauyen da ba’a taba ganin irinsa ba. Kasancewarsu manyan kasashe biyu, yadda Sin da Amurka suke hulda da juna, na haifar da muhimmin tasiri ga makomar dan Adam da ta duniya. Kamar dai yadda mataimakin babban editan jaridar Al-Ahram ta kasar Masar ya fada, “Sin da Amurka kasashe biyu ne mafiya tasiri a duniya, wadanda suke daukar babban nauyi na kiyaye kwanciyar hankali da ci gaba a duniya.” 

To ko ina ne huldar kasashen biyu za ta dosa? Akwai zabi guda biyu a gabansu, na farko shi ne daya ta dage neman nasara daga faduwar dayar, ta rura wutar adawa tsakanin sassa daban daban, kana ta jagoranci duniya zuwa turbar yamutsi da rarrabuwar kawuna; Na biyu kuma shi ne karfafa dunkulewa, da hadin gwiwa da aiki tare, don warware kalubalen da duniya ke fuskanta, da ingiza nasarar tsaro da wadata a duniya. Wadannan zabi 2 na wakiltar alkibla biyu mabambanta, wadanda za su haifar da sakamako biyu masu bambanci da juna.

  • Xi Jinping Ya Tashi Zuwa Kasar Amurka Domin Gudanar Da Taron Shugabannin Kasashen Sin Da Amurka Da Taron APEC Karo Na 30
  • Ganawar San Francisco: Tsaraba Daga Jawabin Shugaba Xi Kan Bukatar Sin Da Amurka Su Nuna Su Manya Ne A Aikace

Hakika, ganawar shugabannin kasashen biyu a ranar 15 ga wata a birnin San Francisco na kasar Amurka, ta samar da amsa game da me ya kamata kasashen biyu suka zaba, wato ya kamata kasashen Sin da Amurka su yi sabon hangen nesa, tare da gina ginshikai biyar tare, don inganta alakar dake tsakaninsu. Na farko, habaka daidaitacciyar fahimta tare, Na biyu, magance rashin jituwa tare yadda ya kamata. Na uku, ciyar da hadin gwiwar moriyar juna gaba tare, sai na hudu, sauke nauyin dake wuyansu a matsayinsu na manyan kasashe. Kana na biyar kuma na karshe, shi ne inganta mu’amala tsakanin al’ummomin kasashen biyu.

Wannan ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai San Francisco ta kasance ziyarar da ya kai kasar ta Amurka bayan tsawon shekaru shida, haka kuma ganawar da ya yi tare takwaransa na Amurka Joe Biden, ta wakana ne biyo bayan ganawar da suka yi a tsibirin Bali na kasar Indonesia a shekarar bara. A yayin ganawarsu, shugaba Xi Jinping ya yi nuni da cewa, “takara tsakanin manyan kasashe masu karfin fada a ji ba ita ce taken wannan zamani ba, kuma ba za ta warware matsalolin Sin da na Amurka da na duniya baki daya ba. Wannan duniya na da fadin da zai wadatar da Sin da Amurka, kuma nasarorinmu damammaki ne gare mu baki daya.”

A hakika, dalilin da ya sa huldar da ke tsakanin Sin da Amurka ta shiga mawuyacin yanayi a shekarun baya shi ne, yadda Amurka ta yi kuskuren daukar Sin din a matsayin babbar abokiyar takara da ta fi yi mata barazana, abin da ya sa ta dauki munanan matakan da ba su dace ba.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Yadda huldar Sin da Amurka za ta bunkasa a hakika ta dogara ne ga yadda kasashen biyu suke fahimtar juna. In dai suna daukar juna a matsayin abokan hadin gwiwa, to, huldarsu za ta yi ta inganta. Amma idan sun dauki juna a matsayin abokan takara, to, za a kara samun yanayi na fito na fito a tsakaninsu.

Ba ma kawai Sin da Amurka za su amfana daga kyakkyawar huldar da ke tsakaninsu ba, har ma da kasashen duniya baki daya. Kamar yadda masanin kasar Senegal kan nazarin harkokin kasar Sin Amadou Diop ya fada, duniya da ke neman karin hadin kai, da bude kofa ga juna, da ma albarka na bukatar a maido da huldar Sin da Amurka kan turbar da ta kamata. “Sin da Amurka dukkansu manyan abokan ciniki ne ga Afirka. Kyakkyawar dangantakar kasashen biyu na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da bunkasar tattalin arziki, da ciniki, da zaman lafiya, da tsaro, da dauwamammen ci gaba a Afirka. Don haka, Afirka na bukatar Sin da Amurka su kara inganta huldarsu.”

A yayin ganawarsu, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kuma jaddada cewa, kamata ya yi a yi la’akari, gami da tsara shirin raya dangantakar Sin da Amurka, ta yin la’akari da makomar dan Adam da ta duniya.

Daga tsibirin Bali har zuwa San Francisco, farfadowar huldar Sin da Amurka ba abu ne mai sauki ba, abubuwan da suka faru sun shaida cewa, muddin dai an tabbatar da daidaiton da shugabannin kasashen biyu suka cimma, za a kai ga kyautata huldar kasashen biyu, kuma duniya na fatan a tabbatar da daidaiton da aka cimma a San Francisco. (Lubabatu Lei)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Usman Baba Pategi (1942 -2023): Rayuwa Da Shahararsa A Fagen Wasan Kwaikwayo

Next Post

Gimbiya Sirindhorn Ta Thailand:Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Inganta Hadin Gwiwar Al’ummun Kasa Da Kasa

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

19 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

20 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

21 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

22 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

23 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

2 days ago
Next Post
Gimbiya Sirindhorn Ta Thailand:Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Inganta Hadin Gwiwar Al’ummun Kasa Da Kasa

Gimbiya Sirindhorn Ta Thailand:Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Inganta Hadin Gwiwar Al’ummun Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.