• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Cin Zarafin Mata Na “EU-UN Spotlight Initiative”: Mun Samu Gagarumin Ci Gaba A Legas – Ibijoke

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Yaki Da Cin Zarafin Mata Na “EU-UN Spotlight Initiative”: Mun Samu Gagarumin Ci Gaba A Legas   – Ibijoke
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan Gwamnan Jihar Legas, Dr. Ibijoke Sanwo-Olu, ta bayyana cewa, sakamakon goyon bayan da suka samu daga shirin Tarayyar Turai (EU) da Majalisar Dinkin Duniya (MDD) na yaki da cin zarafin mata, Jihar Legas ta samu gagarumin ci gaba wajen samar da al’ummar da kowace ‘ya mace za ta iya rayuwa ba tare da tashin hankali ko nuna mata wariya ba.

“Ta hanyar hadin gwiwar da muka yi, mun sami ci gaba sosai wajen samar da al’ummar da kowace mace za ta yi rayuwa ba tare da tashin hankali da wariya ba.” Ta bayyana a wurin rufe shirin na ‘EU-UN Spotlight Initiative’ da aka bullo da shi don kawo karshen cin zarafin mata tare da mika cibiyar da aka samu don wannan aikin ga gwamnatin Jihar Legas a ranar 17 ga Nuwamba 2023.

  • Hukumar Kwastam Ta Kama Kwayoyin Tramadol Na Biliyan N3.55bn A Legas
  • Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

Bikin da aka gudanar a otal din Airport da ke Ikeja ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki da suka hada da kungiyoyin farar hula, daliban Sakandare da dai sauransu.

A cewar Misis Sanwo-Olu, wacce babbar mai ba ta shawara ta musamman kan harkokin cikin gida Misis Motolani Ladipo ta wakilta, Jihar Legas ta ci moriyar hadin gwiwa da kawo sauyi dangane da kawo karshen cin zarafin mata tun bayan kaddamar da shirin na yaki da cin zarafin mata na Tarayyar Turai da Majalisar Dinkin Duniya a shekarar 2019.

“Jihar Legas tare da goyon bayan sashen mata na Majalisar Dinkin Duniya, da UNDP, da UNESCO, UNFPA da kuma UNICEF a karkashin shirin yaki da cin zarafin mata, ta aiwatar da abubuwa da dama da suka shafi ayyukan gwamnati da suka hada da kafa dokoki da tsara manufofi da ke mayar da hankali kan samun adalci ga wadanda suka tsira daga cin zarafin mata.” Ta bayyana.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Uwargidan gwamnan ta yi imani game da nasarar yin aiki tare, inda ta jaddada mahimmancin magance musabbabin cin zarafin mata. Ta kara da cewa, “Bisa himma mai karfi a bangaren rigakafi, kariya, da tabbatar da samun muhimman ayyuka, hadin gwiwa da shirin ‘EU-UN Spotlight Initiative’ yana samar da hanyar da ba za a bar mace babba ko yarinya wajen ci gaba ba a Jihar Legas.”

Kwamishiniyar harkokin mata da yaki da fatara ta Jihar Legas, Ms Cecelia Bolaji Dada, ta bayyana nasarorin da aka samu da kuma muhimman abubuwan da aka cimma a shirin na yaki da cn zarafin mata a Jihar Legas. Ta bayyana yadda suke karfafa ayyuka masu mahimmanci ciki har da kafa asibitocin duba marasa lafiya ta shafin intanet a lokacin annobar COVID19; da karfafa damar samun adalci ga wadanda suka tsira daga cin zarafi, karfafa yekuwar kungiyoyin mata, samar da tallafin gina rayuwa ga wadanda suka tsira daga cin zarafi fiye da 300; da kuma samar da dakin da ake duba wadanda aka ci zarafinsu wanda ya taimaka wajen samar da bayanai a kan shari’ar cin zarafin mata tare da wallafawa a cikin rahoton Ofishin Kididdiga na Kasa.

Babban alkalin jihar Legas, Hon. Kazeem Alogba, ya jaddada muhimmiyar rawar da bangaren shari’a ke takawa wajen magance cin zarafi da nuna wariya ga mata a Jihar Legas.

Da yake magana ta bakin Mai shari’a Abiola Soladoye, ya bayyana mahimmancin kin yin shiru kan abubuwan da suka shafi cin zarafi tare da karfafa wa wadanda suka tsira daga aika-aikar su rika neman adalci ba tare da tsoro ba.

“Bai kamata a yi watsi da miyagun laifukan da ake wa mata ba, kuma idan aka ba da rahoton, wadanda abin ya shafa ka da su yi shakka su fito su fada.” Yana mai bayyana cewa, “‘Yansanda suna da ruwa da tsaki tare da bangaren shari’a wajen taimaka wa dakile lamuran da suka shafi cin zarafin mata.”

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Legas, Mudashiru Obasa, ya jaddada kudirin majalisar na yakar duk wani nau’in cin zarafin mata a jihar.

Wanda Hon. Princess Omolara Oyekan ta wakilta, shugaban majalisar ya jaddada cewa, “Majalisar ba ta daukar duk wani nau’i na cin zarafin mata ta kowace hanya da sanya, sannan kafa hukumar yaki da cin zarafin mata ta Jihar Legas wani muhimmin mataki ne na sadaukarwar da majalisar ta yi don kawar da cin zarafin”.

Ya kara da cewa kokarin da majalisar dokokin Jihar Legas ta yi na samar da dokoki na kare hakkin mata ya sa manyan hukumomi irin su hukumar yaki da cin zarafin mata ta jihar Legas da ma’aikatar mata ta jihar Legas suka yi tsayin daka tare da tsre wa tsara kan kare hakkokin mata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LegasYaki da cin zarafin mata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gavi Ya Samu Mummunan Rauni A Tawagar Spaniya

Next Post

Red Cross Ta Yi Sabbin Shugabanni A Adamawa

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

2 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

14 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

19 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

20 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

21 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

22 hours ago
Next Post
Red Cross Ta Yi Sabbin Shugabanni A Adamawa

Red Cross Ta Yi Sabbin Shugabanni A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.