ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Cin Zarafin Mata Na “EU-UN Spotlight Initiative”: Mun Samu Gagarumin Ci Gaba A Legas – Ibijoke

by Leadership Hausa
3 years ago
Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Legas, Dr. Ibijoke Sanwo-Olu, ta bayyana cewa, sakamakon goyon bayan da suka samu daga shirin Tarayyar Turai (EU) da Majalisar Dinkin Duniya (MDD) na yaki da cin zarafin mata, Jihar Legas ta samu gagarumin ci gaba wajen samar da al’ummar da kowace ‘ya mace za ta iya rayuwa ba tare da tashin hankali ko nuna mata wariya ba.

“Ta hanyar hadin gwiwar da muka yi, mun sami ci gaba sosai wajen samar da al’ummar da kowace mace za ta yi rayuwa ba tare da tashin hankali da wariya ba.” Ta bayyana a wurin rufe shirin na ‘EU-UN Spotlight Initiative’ da aka bullo da shi don kawo karshen cin zarafin mata tare da mika cibiyar da aka samu don wannan aikin ga gwamnatin Jihar Legas a ranar 17 ga Nuwamba 2023.

  • Hukumar Kwastam Ta Kama Kwayoyin Tramadol Na Biliyan N3.55bn A Legas
  • Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

Bikin da aka gudanar a otal din Airport da ke Ikeja ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki da suka hada da kungiyoyin farar hula, daliban Sakandare da dai sauransu.

ADVERTISEMENT

A cewar Misis Sanwo-Olu, wacce babbar mai ba ta shawara ta musamman kan harkokin cikin gida Misis Motolani Ladipo ta wakilta, Jihar Legas ta ci moriyar hadin gwiwa da kawo sauyi dangane da kawo karshen cin zarafin mata tun bayan kaddamar da shirin na yaki da cin zarafin mata na Tarayyar Turai da Majalisar Dinkin Duniya a shekarar 2019.

“Jihar Legas tare da goyon bayan sashen mata na Majalisar Dinkin Duniya, da UNDP, da UNESCO, UNFPA da kuma UNICEF a karkashin shirin yaki da cin zarafin mata, ta aiwatar da abubuwa da dama da suka shafi ayyukan gwamnati da suka hada da kafa dokoki da tsara manufofi da ke mayar da hankali kan samun adalci ga wadanda suka tsira daga cin zarafin mata.” Ta bayyana.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Uwargidan gwamnan ta yi imani game da nasarar yin aiki tare, inda ta jaddada mahimmancin magance musabbabin cin zarafin mata. Ta kara da cewa, “Bisa himma mai karfi a bangaren rigakafi, kariya, da tabbatar da samun muhimman ayyuka, hadin gwiwa da shirin ‘EU-UN Spotlight Initiative’ yana samar da hanyar da ba za a bar mace babba ko yarinya wajen ci gaba ba a Jihar Legas.”

Kwamishiniyar harkokin mata da yaki da fatara ta Jihar Legas, Ms Cecelia Bolaji Dada, ta bayyana nasarorin da aka samu da kuma muhimman abubuwan da aka cimma a shirin na yaki da cn zarafin mata a Jihar Legas. Ta bayyana yadda suke karfafa ayyuka masu mahimmanci ciki har da kafa asibitocin duba marasa lafiya ta shafin intanet a lokacin annobar COVID19; da karfafa damar samun adalci ga wadanda suka tsira daga cin zarafi, karfafa yekuwar kungiyoyin mata, samar da tallafin gina rayuwa ga wadanda suka tsira daga cin zarafi fiye da 300; da kuma samar da dakin da ake duba wadanda aka ci zarafinsu wanda ya taimaka wajen samar da bayanai a kan shari’ar cin zarafin mata tare da wallafawa a cikin rahoton Ofishin Kididdiga na Kasa.

Babban alkalin jihar Legas, Hon. Kazeem Alogba, ya jaddada muhimmiyar rawar da bangaren shari’a ke takawa wajen magance cin zarafi da nuna wariya ga mata a Jihar Legas.

Da yake magana ta bakin Mai shari’a Abiola Soladoye, ya bayyana mahimmancin kin yin shiru kan abubuwan da suka shafi cin zarafi tare da karfafa wa wadanda suka tsira daga aika-aikar su rika neman adalci ba tare da tsoro ba.

“Bai kamata a yi watsi da miyagun laifukan da ake wa mata ba, kuma idan aka ba da rahoton, wadanda abin ya shafa ka da su yi shakka su fito su fada.” Yana mai bayyana cewa, “‘Yansanda suna da ruwa da tsaki tare da bangaren shari’a wajen taimaka wa dakile lamuran da suka shafi cin zarafin mata.”

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Legas, Mudashiru Obasa, ya jaddada kudirin majalisar na yakar duk wani nau’in cin zarafin mata a jihar.

Wanda Hon. Princess Omolara Oyekan ta wakilta, shugaban majalisar ya jaddada cewa, “Majalisar ba ta daukar duk wani nau’i na cin zarafin mata ta kowace hanya da sanya, sannan kafa hukumar yaki da cin zarafin mata ta Jihar Legas wani muhimmin mataki ne na sadaukarwar da majalisar ta yi don kawar da cin zarafin”.

Ya kara da cewa kokarin da majalisar dokokin Jihar Legas ta yi na samar da dokoki na kare hakkin mata ya sa manyan hukumomi irin su hukumar yaki da cin zarafin mata ta jihar Legas da ma’aikatar mata ta jihar Legas suka yi tsayin daka tare da tsre wa tsara kan kare hakkokin mata.

Mata
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Red Cross Ta Yi Sabbin Shugabanni A Adamawa

Red Cross Ta Yi Sabbin Shugabanni A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.