ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Cin Zarafin Mata Na “EU-UN Spotlight Initiative”: Mun Samu Gagarumin Ci Gaba A Legas – Ibijoke

by Leadership Hausa
3 years ago
Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Legas, Dr. Ibijoke Sanwo-Olu, ta bayyana cewa, sakamakon goyon bayan da suka samu daga shirin Tarayyar Turai (EU) da Majalisar Dinkin Duniya (MDD) na yaki da cin zarafin mata, Jihar Legas ta samu gagarumin ci gaba wajen samar da al’ummar da kowace ‘ya mace za ta iya rayuwa ba tare da tashin hankali ko nuna mata wariya ba.

“Ta hanyar hadin gwiwar da muka yi, mun sami ci gaba sosai wajen samar da al’ummar da kowace mace za ta yi rayuwa ba tare da tashin hankali da wariya ba.” Ta bayyana a wurin rufe shirin na ‘EU-UN Spotlight Initiative’ da aka bullo da shi don kawo karshen cin zarafin mata tare da mika cibiyar da aka samu don wannan aikin ga gwamnatin Jihar Legas a ranar 17 ga Nuwamba 2023.

  • Hukumar Kwastam Ta Kama Kwayoyin Tramadol Na Biliyan N3.55bn A Legas
  • Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

Bikin da aka gudanar a otal din Airport da ke Ikeja ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki da suka hada da kungiyoyin farar hula, daliban Sakandare da dai sauransu.

ADVERTISEMENT

A cewar Misis Sanwo-Olu, wacce babbar mai ba ta shawara ta musamman kan harkokin cikin gida Misis Motolani Ladipo ta wakilta, Jihar Legas ta ci moriyar hadin gwiwa da kawo sauyi dangane da kawo karshen cin zarafin mata tun bayan kaddamar da shirin na yaki da cin zarafin mata na Tarayyar Turai da Majalisar Dinkin Duniya a shekarar 2019.

“Jihar Legas tare da goyon bayan sashen mata na Majalisar Dinkin Duniya, da UNDP, da UNESCO, UNFPA da kuma UNICEF a karkashin shirin yaki da cin zarafin mata, ta aiwatar da abubuwa da dama da suka shafi ayyukan gwamnati da suka hada da kafa dokoki da tsara manufofi da ke mayar da hankali kan samun adalci ga wadanda suka tsira daga cin zarafin mata.” Ta bayyana.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Uwargidan gwamnan ta yi imani game da nasarar yin aiki tare, inda ta jaddada mahimmancin magance musabbabin cin zarafin mata. Ta kara da cewa, “Bisa himma mai karfi a bangaren rigakafi, kariya, da tabbatar da samun muhimman ayyuka, hadin gwiwa da shirin ‘EU-UN Spotlight Initiative’ yana samar da hanyar da ba za a bar mace babba ko yarinya wajen ci gaba ba a Jihar Legas.”

Kwamishiniyar harkokin mata da yaki da fatara ta Jihar Legas, Ms Cecelia Bolaji Dada, ta bayyana nasarorin da aka samu da kuma muhimman abubuwan da aka cimma a shirin na yaki da cn zarafin mata a Jihar Legas. Ta bayyana yadda suke karfafa ayyuka masu mahimmanci ciki har da kafa asibitocin duba marasa lafiya ta shafin intanet a lokacin annobar COVID19; da karfafa damar samun adalci ga wadanda suka tsira daga cin zarafi, karfafa yekuwar kungiyoyin mata, samar da tallafin gina rayuwa ga wadanda suka tsira daga cin zarafi fiye da 300; da kuma samar da dakin da ake duba wadanda aka ci zarafinsu wanda ya taimaka wajen samar da bayanai a kan shari’ar cin zarafin mata tare da wallafawa a cikin rahoton Ofishin Kididdiga na Kasa.

Babban alkalin jihar Legas, Hon. Kazeem Alogba, ya jaddada muhimmiyar rawar da bangaren shari’a ke takawa wajen magance cin zarafi da nuna wariya ga mata a Jihar Legas.

Da yake magana ta bakin Mai shari’a Abiola Soladoye, ya bayyana mahimmancin kin yin shiru kan abubuwan da suka shafi cin zarafi tare da karfafa wa wadanda suka tsira daga aika-aikar su rika neman adalci ba tare da tsoro ba.

“Bai kamata a yi watsi da miyagun laifukan da ake wa mata ba, kuma idan aka ba da rahoton, wadanda abin ya shafa ka da su yi shakka su fito su fada.” Yana mai bayyana cewa, “‘Yansanda suna da ruwa da tsaki tare da bangaren shari’a wajen taimaka wa dakile lamuran da suka shafi cin zarafin mata.”

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Legas, Mudashiru Obasa, ya jaddada kudirin majalisar na yakar duk wani nau’in cin zarafin mata a jihar.

Wanda Hon. Princess Omolara Oyekan ta wakilta, shugaban majalisar ya jaddada cewa, “Majalisar ba ta daukar duk wani nau’i na cin zarafin mata ta kowace hanya da sanya, sannan kafa hukumar yaki da cin zarafin mata ta Jihar Legas wani muhimmin mataki ne na sadaukarwar da majalisar ta yi don kawar da cin zarafin”.

Ya kara da cewa kokarin da majalisar dokokin Jihar Legas ta yi na samar da dokoki na kare hakkin mata ya sa manyan hukumomi irin su hukumar yaki da cin zarafin mata ta jihar Legas da ma’aikatar mata ta jihar Legas suka yi tsayin daka tare da tsre wa tsara kan kare hakkokin mata.

Mata
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Red Cross Ta Yi Sabbin Shugabanni A Adamawa

Red Cross Ta Yi Sabbin Shugabanni A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.