• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasafin Kuɗin 2024: A Jihar Katsina, Ɓangaren Noma Zai Samu Kashi 6.21% Kawai – Kwamishina.

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Kasafin Kuɗin 2024: A Jihar Katsina, Ɓangaren Noma Zai Samu Kashi 6.21% Kawai – Kwamishina.
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Katsina ta bayyana cewa ɓangaren noma zai samu kaso 6.21 cikin 100 na kasafin Kuɗin shekarar 2024 da gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya gabatar a gaban zauren Majalisar dokokin jihar Katsina.

Kwamishinan kasafin kudi da tsare-tsare na jihar Katsina, Alhaji Bello Kagara ya bayyana haka ga manema labarai a Katsina.

  • Gwamna Abba Yusuf Ya Nada Sabon Shugaban Ma’aikatan Gwamnati
  • Za Mu Samar Da Wutar Lantarki MW60 Ko Sola MW50 A Kowace Jiha -Gwamnonin Arewa Maso-Gabas

Kwamishinan ya ce, gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya tabbatar da kasafin kudin shekarar 2024 na Naira biliyan 454,308,862,113.96 amma ɓangaren ya samu naira biliyan 20, 513,909,753.71 inda haka ke nuna ya samu kaso 6.21%.

Haka kuma ya ƙara da cewa akwai manyan ayyuka da ake sa ran zasu lakume biliyoyin nairori a cikin kasafin shekarar 2024 da suka haɗa da ɓangaren Ruwan Sha da Ilimi da Kiwon lafiya da Ayyuka da Muhalli sai kuma noma.

” Bangaren ruwan sha ana sa ran zai lakume kimanin naira biliyan 67,161,802,447.39 inda yake wakilcin kaso 20.35% sai kuma ɓangaren ilimi da zai lakume naira biliyan 66,422,889,400.21 shima yana wakilcin kaso 20.13%” inji shi

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Sauran ɓangarori sun haɗa da ma’aikatar ayyuka inda za a kashe kimanin naira biliyan 53,484,733,251.59 bisa wakilcin kaso 16.20% cikin ɗari, sai harkar kiwon lafiya ana sa ran zata kuɗi wuri na gugar wuri har naira biliyan 38,326, 421,172.23 cikin ɗari inda ta samu wakilcin kaso 11.43%.

Alhaji Bello Kagara ya cigaba da bayanin cewa ɓangaren muhalli zai samo naira biliyan 37,700,909,753.24 kaso 11.43% cikin ɗari wanda jumlar kuɗin suka kasance Naira biliyan 282,607,873,235.37

Tunda farko da yake jawabin sa Kwamishinan ya ce kasafin Kuɗin wannan shekarar na 2024 ya ɗararwa na bara da kimanin biliyan 153,675,604,150.96 daidai da kaso 51.11%

Kazalika Alhaji Bello Kagara ya ce wannan kasafin kudi na shekarar 2024 mai taken ‘Gina Gobe’ za a aiwatar da shi da waɗannan hanyoyin kuɗaɗen shiga.

A cewar Kwamishinan ana sa ran samun kuɗaɗen shiga daga hukumar tattara kuɗaɗen shiga ta jihar Katsina da ma’aikatu da hukumomin gwamnati inda ake sa ran samun kimanin naira biliyan 25,826,650,462.67 sai kuma kuɗaɗen da wasu hukumomin gwamnati za su samar da suka kai kimanin naira biliyan 14,173,349,537.33

Sai kuma ya kara da cewa akwai kuɗaɗen da ake sa ran samu daga ɓangaren rabon arzikin ƙasa kimanin naira biliyan 148,061,977,186.28 da sauran ɓangarori na kuɗaɗen shiga.

Wannan kasafin kudi na shekarar 2024 bangaren ayyukan yau da kullum zai lashe kimanin naira biliyan 124,329,343,517.99 sai kuma manyan ayyuka za su kashi naira biliyan 329,979,518,595.97 jumla naira biliyan 454,308,862,113.96.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwaman KatsinaKasafin kudin jihar KatsinaNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ribar Masana’antun Sin Ta Karu A Watan Oktoba

Next Post

Nijeriya Ta Nanatawa Amurka Kudirinta Na Ci Gaba Baiwa ‘Yan Jarida ‘Yanci

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

3 hours ago
Noma
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

5 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

8 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

11 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

11 hours ago
Next Post
Amurka

Nijeriya Ta Nanatawa Amurka Kudirinta Na Ci Gaba Baiwa 'Yan Jarida 'Yanci

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Noma

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.