• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Fuskantar Karancin Kayan Noma

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Nijeriya Na Fuskantar Karancin Kayan Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Wasu jami’an gwamnati da na kamfanoni, sun bayyana sama da kashi 70 cikin dari na al’ummar kasar nan a matsayin wadanda suka dogara da fannin aikin noma, sai dai abin takaicin shi ne, Nijeriya na fuskantar kalubalen rashin wadatattun kayan aikin noma na zamani, wanda hakan ke jawo wa fannin aikin noman koma baya. 

Wata kididdiga da bankin duniya ya yi a kan harkar aikin noman a kasar nan, ya tabbatar da cewa; taraktocin da Nijeriya ta mallaka don yin noma bai haura 45,000 kacal ba, mai makon akalla guda 81,000 don aiwatar da harkokin noman.

  • Gwamna Uba Sani Ya Kafa Kwamitin Binciken Matsalolin Aiki Hajji
  • Basirar Henry Kissinger Abu Mai Daraja Ne Ga Amurka

Haka zalika, yanzu haka a kasar nan akwai akalla famfunan ban ruwan noman rani sama da 200,000 da sauran makamantansu.

Sannan, Nijeriya na da fadin kasar noma kuma ingantacciya kimanin 8,000, wanda hakan ke nuna cewa; kasar na da kimanin kadadar noma kimanin miliyan 80.

Bugu da kari, a cewar wani rahoton bankin duniya, bangaren gwamnati na shigo da akalla kashi 90 a cikin 100 na taraktocin noma cikin kasar nan, wanda kuma Ma’aikatar Aikin Noma da Raya Karkarar ce ke karbar wannan adadi, sannan mafi akasarinsu, kananan taraktoci ne.

Kazalika rahoton ya kara da cewa, bangaren kamfanoni masu zaman kansu, na shigo da taraktoci zuwa cikin kasar nan akalla kashi 10 cikin 100 a duk shekara.

Har ila yau, wadannan taraktocin noma na kai wa tsawon shekaru bakwai kafin su daina aiki, amma ya danganta da irin yadda samfurin taraktar ya ke.

Wakazalika, an kiyasta cewa sama da taraktocin noma 200 ne ke daina aiki duk da cewa, a duk shekara ana shigo da kimanin 1,000 Nijeriya.

Sai dai, domin kokarin lalubo mafita a kan karancin taraktocin, a kwanakin baya, Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, ta kulla yarjejeniya da  kamfanin John Deere da ke kera taraktoci, domin samar da akalla taraktoci 2,000 ga wannan kasa, musamman domin a kara bunkasa fannin aikin noma na zamani.

Haka nan, ana sa ran wannan yarjejeniya da aka kulla; za ta kai tsawon shekaru biyar, wanda a karkashin yarjejeniyar za a samar wa Nijeriya taraktoci 10,000.

Ministan Aikin Noma da Samar da Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya bayyana cewa, Nijeriya na fuskantar matukar karancin kayan aikin noma na zamani.

Kyari ya kara da cewa, ma’aikatarsa ta kulla yarjejeniya da kamfanin kera taraktoci na John Deere, domin samar da taraktoci sama da 2,000 a kan farashi mai sauki, don hakan ya bai wa kananan manoma samun damar siya a fadin wannan kasa baki-daya.

A cewar tasa, an samu damar kulla wannan yarjejeniya ce, biyo bayan wata ganawa a kwanakin baya da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya yi da wasu manyan jami’ai na Kamfanin John Deere a Kasar Amurka.

Wannan yarjejeniya, za ta kuma bai wa Kamfanin John Deere da abokan hadakar damar kafa masana’antar hada taraktoci a kasar nan, wadda bayan an sayi taraktocin; za kuma a dangana da su ga manoma kai tsaye.

Wakazalika, kwararru a fannin aikin noma a kasar nan, sun yi fatan dorewar wannan yarjejeniya, musamman ganin Ma’aikatar Aikin Noma a baya ta sha kulla ire-iren wannan yarjejeniya; amma sai ta gaza cimma burin da ta sanya a gaba.

Mista Jason Brantley, Mataimakin Shugaba a Kamfanin John Deere, ya bayyana jin dadinsa na shirin kafa kamfanin hada taraktocin noma a kasar nan.

Brantley ya sanar da cewa, kamfanin ya mayar da hankali ne wajen lalubo da mafita a kan kalubalen da kananan manoma ke fuskanta tare da habaka aikin noma da kayan aiki na zamani.

A cewarsa, Kamfanin John Deere ya mayar da hankali ne a kan yin noma da kayan aiki na zamani, domin aiwatar da aikin na noma mai tarin yawa a kadadar noma tare da kara bunkasa samar da wadataccen abinci a fadin kasar nan baki-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Samar Da Kundin Tattara Bayanai Na Ilimi

Next Post

Dusar Kankara Ta Sa An Dage Wasan Bayern Munich Da Union Berlin

Related

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

4 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

2 weeks ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

2 weeks ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

2 weeks ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

3 weeks ago
Next Post
Dusar Kankara Ta Sa An Dage Wasan Bayern Munich Da Union Berlin

Dusar Kankara Ta Sa An Dage Wasan Bayern Munich Da Union Berlin

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

July 3, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3

July 3, 2025
Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

July 3, 2025
Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.